< Zabura 38 >
1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Un psaume de David, pour un mémorial. Yahvé, ne me réprimande pas dans ta colère, et ne me châtie pas dans ton vif mécontentement.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Car tes flèches m'ont transpercé, ta main s'appuie fortement sur moi.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Il n'y a pas de solidité dans ma chair, à cause de ton indignation, il n'y a pas non plus de santé dans mes os à cause de mon péché.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Car mes iniquités ont passé par-dessus ma tête. Comme un lourd fardeau, ils sont trop lourds pour moi.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mes blessures sont répugnantes et corrompues. à cause de ma bêtise.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Je souffre et je suis très abattu. Je suis en deuil toute la journée.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Car ma taille est remplie de feu. Il n'y a pas de solidité dans ma chair.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Je suis faible et gravement meurtri. J'ai gémi à cause de l'angoisse de mon cœur.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Seigneur, tout mon désir est devant toi. Mes gémissements ne te sont pas cachés.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mon cœur palpite. Mes forces m'abandonnent. Quant à la lumière de mes yeux, elle m'a aussi quitté.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Mes amants et mes amis se tiennent à l'écart de mon fléau. Mes proches sont loin.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Ceux qui en veulent à ma vie me tendent des pièges. Ceux qui cherchent à me faire du mal disent des choses malicieuses, et méditer des tromperies toute la journée.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Mais moi, comme un sourd, je n'entends pas. Je suis comme un homme muet qui n'ouvre pas la bouche.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Oui, je suis comme un homme qui n'entend pas, dans la bouche duquel il n'y a pas de réprimandes.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Car j'espère en toi, Yahvé. Tu répondras, Seigneur mon Dieu.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Car j'ai dit: « Ne les laisse pas se réjouir à mon sujet, ou s'exaltent au-dessus de moi quand mon pied glisse. »
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Car je suis prêt à tomber. Ma douleur est continuellement devant moi.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Car je vais déclarer mon iniquité. Je serai désolé pour mon péché.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Mais mes ennemis sont vigoureux et nombreux. Ceux qui me détestent sans raison sont nombreux.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Ceux qui rendent le mal pour le bien sont aussi des adversaires pour moi, parce que je suis ce qui est bon.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Ne m'abandonne pas, Yahvé. Mon Dieu, ne t'éloigne pas de moi.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Dépêchez-vousde m'aider, Seigneur, mon salut.