< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
A Psalm of David, to bring to remembrance. O LORD, rebuke me not in thy wrath: neither chasten me in thy hot displeasure.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
For thy arrows stick fast in me, and thy hand falleth heavy upon me.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
[There is] no soundness in my flesh because of thy anger; neither [is there any] rest in my bones because of my sin.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
For my iniquities have gone over my head: as a heavy burden they are too heavy for me.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
My wounds are offensive, [and] are corrupt because of my foolishness.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
I am troubled; I am bowed down greatly; I go mourning all the day long.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
For my loins are filled with a lothsome [disease]: and [there is] no soundness in my flesh.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
I am feeble and grievously broken: I have roared by reason of the disquietness of my heart.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
LORD, all my desire [is] before thee; and my groaning is not hid from thee.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
My heart panteth, my strength faileth me: as for the light of my eyes, that also is gone from me.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
My lovers and my friends stand aloof from my affliction; and my kinsmen stand afar off.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
They also that seek after my life lay snares [for me]: and they that seek my hurt speak mischievous things, and imagine deceits all the day long.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
But I, as a deaf [man], heard not; and [I was] as a dumb man [that] openeth not his mouth.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Thus I was as a man that heareth not, and in whose mouth [are] no reproofs.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
For in thee, O LORD, do I hope: thou wilt hear, O LORD my God.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
For I said, [Hear me], lest [otherwise] they should rejoice over me: when my foot slippeth, they magnify [themselves] against me.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
For I [am] ready to halt, and my sorrow [is] continually before me.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
For I will declare my iniquity; I will be sorry for my sin.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
But my enemies [are] lively, [and] they are strong: and they that hate me wrongfully are multiplied.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
They also that render evil for good are my adversaries; because I follow [the thing that is] good.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Forsake me not, O LORD: O my God, be not far from me.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Make haste to help me, O LORD my salvation.

< Zabura 38 >