< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
O lord, rebuke me not in your wrath: neither chasten me in your hot displeasure.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
For your arrows stick fast in me, and your hand presses me sore.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
There is no soundness in my flesh because of your anger; neither is there any rest in my bones because of my sin.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
For mine iniquities are gone over mine head: as an heavy burden they are too heavy for me.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
My wounds stink and are corrupt because of my foolishness.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
I am troubled; I am bowed down greatly; I go mourning all the day long.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
For my loins are filled with a loathsome disease: and there is no soundness in my flesh.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
I am feeble and sore broken: I have roared by reason of the chaos of my heart.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Lord, all my desire is before you; and my groaning is not hid from you.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
My heart pants, my strength fails me: as for the light of mine eyes, it also is gone from me.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
My lovers and my friends stand aloof from my sore; and my kinsmen stand far off.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
They also that seek after my life lay snares for me: and they that seek my hurt speak mischievous things, and imagine deceits all the day long.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
But I, as a deaf man, heard not; and I was as a dumb man that opens not his mouth.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Thus I was as a man that hears not, and in whose mouth are no reproofs.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
For in you, O LORD, do I hope: you will hear, O Lord my God.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
For I said, Hear me, lest otherwise they should rejoice over me: when my foot slips, they magnify themselves against me.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
For I am ready to halt, and my sorrow is continually before me.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
For I will declare mine iniquity; I will be sorry for my sin.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
But mine enemies are lively, and they are strong: and they that hate me wrongfully are multiplied.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
They also that render evil for good are mine adversaries; because I follow the thing that good is.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Forsake me not, O LORD: O my God, be not far from me.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Make haste to help me, O Lord my salvation.

< Zabura 38 >