< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
A psalm for David, for a remembrance of the sabbath. Rebuke me not, O Lord, in thy indignation; nor chastise me in thy wrath.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
For thy arrows are fastened in me: and thy hand hath been strong upon me.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
There is no health in my flesh, because of thy wrath: there is no peace for my bones, because of my sins.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
For my iniquities are gone over my head: and as a heavy burden are become heavy upon me.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
My sores are putrified and corrupted, because of my foolishness.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
I am become miserable, and am bowed down even to the end: I walked sorrowful all the day long.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
For my loins are filled with illusions; and there is no health in my flesh.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
I am afflicted and humbled exceedingly: I roared with the groaning of my heart.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Lord, all my desire is before thee, and my groaning is not hidden from thee.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
My heart is troubled, my strength hath left me, and the light of my eyes itself is not with me.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
My friends and my neighbours have drawn near, and stood against me. And they that were near me stood afar off:
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
And they that sought my soul used violence. And they that sought evils to me spoke vain things, and studied deceits all the day long.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
But I, as a deaf man, heard not: and as a dumb man not opening his mouth.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
And I became as a man that heareth not: and that hath no reproofs in his mouth.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
For in thee, O Lord, have I hoped: thou wilt hear me, O Lord my God.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
For I said: Lest at any time my enemies rejoice over me: and whilst my feet are moved, they speak great things against me.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
For I am ready for scourges: and my sorrow is continually before me.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
For I will declare my inequity: and I will think for my sin.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
But my enemies live, and are stronger that I: and they hate me wrongfully are multiplied.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
They that render evil for good, have detracted me, because I followed goodness.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Forsake me not, O Lord my God: do not thou depart from me.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Attend unto my help, O Lord, the God of my salvation.

< Zabura 38 >