< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Van David; bij het herinneringsoffer. Jahweh, tuchtig mij niet in uw toorn, Kastijd mij niet in uw gramschap:
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Want uw pijlen hebben mij getroffen, Uw hand drukt zwaar op mij neer.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Er is geen gezonde plek aan mijn vlees om uw toorn, Niets gaafs aan mijn gebeente om mijn zonden;
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Want mijn misdaden stapelen zich op mijn hoofd, En drukken mij neer als een loodzware last.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mijn wonden stinken en dragen Om mijn verdwazing;
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Ik ga gebukt en geknakt, Loop heel de dag maar treurend rond.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Mijn lenden zijn aan alle kanten ontstoken, Geen gezonde plek aan mijn vlees;
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Ik ben uitgeput en gebroken, En snik het uit door het gekerm van mijn hart.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Heer, al mijn jammeren is U bekend, Mijn zuchten voor U niet verborgen;
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Wild bonst mijn hart, de kracht ontzinkt mij, Zelfs het licht van mijn ogen is heen.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Mijn vrienden en makkers keren zich af om mijn plagen, En mijn verwanten staan op een afstand te spotten;
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Die mijn leven belagen en mijn ongeluk zoeken, Bespreken mijn val, en belasteren mij de hele dag.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Maar ik ben als een dove, die het niet hoort, Als een stomme, die zijn mond niet opent,
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Als een man, die niet luistert, En wiens mond geen antwoord meer weet.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Neen, Jahweh, ik verlaat mij op U: Antwoord Gij, mijn Heer en mijn God;
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Want ik vrees, dat men zich vrolijk over mij maakt, Een grote mond tegen mij zet, nu mijn voeten wankelen.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Ja, ieder ogenblik dreig ik te vallen, Mijn ellende staat mij steeds voor de geest;
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Want ik moet wel mijn misdaad bekennen, En bekommerd zijn over mijn schuld.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
En machtig zijn ook, die zonder reden mijn vijanden zijn, Talrijk, die mij onverdiend haten,
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Die goed vergelden met kwaad, Mij ondanks mijn beste bedoeling bestrijden.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Jahweh, verlaat mij dus niet; Mijn God, blijf niet verre van mij!
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Kom mij spoedig te hulp, Mijn Heer en mijn Heil!

< Zabura 38 >