< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
(En salme af David. Lehazkir.) HERRE, revs mig ej i din vrede, tugt mig ej i din Harme!
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Thi dine pile sidder i mig, din Hånd har lagt sig på mig.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Intet er karskt på min Krop for din Vredes Skyld, intet uskadt i mine Ledemod for mine Synders Skyld;
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
thi over mit Hoved skyller min Brøde som en tyngende Byrde, for tung for mig.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mine Sår både stinker og rådner, for min Dårskabs Skyld går jeg bøjet;
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
jeg er såre nedtrykt, sorgfuld vandrer jeg Dagen lang.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Thi Lænderne er fulde af Brand, intet er karskt på min Krop,
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
jeg er lammet og fuldkommen knust, jeg skriger i Hjertets Vånde.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
HERRE, du kender al min Attrå, mit Suk er ej skjult for dig;
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
mit Hjerte banker, min Kraft har svigtet, selv mit Øje har mistet sin Glans.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
For min Plages Skyld flyr mig Ven og Frænde, mine Nærmeste holder sig fjert;
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
de, der vil mig til Livs, sætter Snarer, og de, der vil mig ondt, lægger Råd om Fordærv, de tænker Dagen igennem på Svig.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Men jeg er som en døv, der intet hører, som en stum, der ej åbner sin Mund,
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
som en Mand, der ikke kan høre, i hvis Mund der ikke er Svar.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Thi til dig står mit Håb, o HERRE, du vil bønhøre, Herre min Gud,
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
når jeg siger: "Lad dem ikke glæde sig over mig, hovmode sig over min vaklende Fod!"
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Thi jeg står allerede for Fald, mine Smerter minder mig stadig;
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
thi jeg må bekende min Skyld må sørge over min Synd.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Mange er de, der med Urette er mine Fjender, talrige de, der hader mig uden Grund,
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
som lønner mig godt med ondt, som står mig imod, fordi jeg søger det gode.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
HERRE, forlad mig ikke, min Gud, hold dig ikke borte fra mig,
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
il mig til Hjælp, o Herre, min Frelse!

< Zabura 38 >