< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
En Salme af David. Lehazkir.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
HERRE, revs mig ej i din Vrede, tugt mig ej i din Harme!
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Thi dine Pile sidder i mig, din Haand har lagt sig paa mig.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Intet er karskt paa min Krop for din Vredes Skyld, intet uskadt i mine Ledemod for mine Synders Skyld;
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
thi over mit Hoved skyller min Brøde som en tyngende Byrde, for tung for mig.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Mine Saar baade stinker og raadner, for min Daarskabs Skyld gaar jeg bøjet;
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
jeg er saare nedtrykt, sorgfuld vandrer jeg Dagen lang.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Thi Lænderne er fulde af Brand, intet er karskt paa min Krop,
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
jeg er lammet og fuldkommen knust, jeg skriger i Hjertets Vaande.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
HERRE, du kender al min Attraa, mit Suk er ej skjult for dig;
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
mit Hjerte banker, min Kraft har svigtet, selv mit Øje har mistet sin Glans.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
For min Plages Skyld flyr mig Ven og Frænde, mine Nærmeste holder sig fjernt;
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
de, der vil mig til Livs, sætter Snarer, og de, der vil mig ondt, lægger Raad om Fordærv, de tænker Dagen igennem paa Svig.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Men jeg er som en døv, der intet hører, som en stum, der ej aabner sin Mund,
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
som en Mand, der ikke kan høre, i hvis Mund der ikke er Svar.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Thi til dig staar mit Haab, o HERRE, du vil bønhøre, Herre min Gud,
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
naar jeg siger: »Lad dem ikke glæde sig over mig, hovmode sig over min vaklende Fod!«
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Thi jeg staar allerede for Fald, mine Smerter minder mig stadig;
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
thi jeg maa bekende min Skyld, maa sørge over min Synd.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Mange er de, der med Urette er mine Fjender, talrige de, der hader mig uden Grund,
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
som lønner mig godt med ondt, som staar mig imod, fordi jeg søger det gode.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
HERRE, forlad mig ikke, min Gud, hold dig ikke borte fra mig, il mig til Hjælp, o Herre, min Frelse!

< Zabura 38 >