< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
大衛的紀念詩。 耶和華啊,求你不要在怒中責備我, 不要在烈怒中懲罰我!
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
因為,你的箭射入我身; 你的手壓住我。
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
因你的惱怒,我的肉無一完全; 因我的罪過,我的骨頭也不安寧。
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
我的罪孽高過我的頭, 如同重擔叫我擔當不起。
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
因我的愚昧, 我的傷發臭流膿。
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
我疼痛,大大拳曲, 終日哀痛。
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
我滿腰是火; 我的肉無一完全。
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
我被壓傷,身體疲倦; 因心裏不安,我就唉哼。
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
主啊,我的心願都在你面前; 我的歎息不向你隱瞞。
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
我心跳動,我力衰微, 連我眼中的光也沒有了。
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
我的良朋密友因我的災病都躲在旁邊站着; 我的親戚本家也遠遠地站立。
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
那尋索我命的設下網羅; 那想要害我的口出惡言, 終日思想詭計。
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
但我如聾子不聽, 像啞巴不開口。
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
我如不聽見的人, 口中沒有回話。
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
耶和華啊,我仰望你! 主-我的上帝啊,你必應允我!
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
我曾說:恐怕他們向我誇耀; 我失腳的時候,他們向我誇大。
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
我幾乎跌倒; 我的痛苦常在我面前。
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
我要承認我的罪孽; 我要因我的罪憂愁。
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
但我的仇敵又活潑又強壯, 無理恨我的增多了。
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
以惡報善的與我作對, 因我是追求良善。
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
耶和華啊,求你不要撇棄我! 我的上帝啊,求你不要遠離我!
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
拯救我的主啊,求你快快幫助我!

< Zabura 38 >