< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
No te impacientes a causa de los malignos, Ni tengas envidia de los que hacen iniquidad.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Porque como hierba, serán pronto marchitados, Y como la hierba verde se secarán.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Confía en Yavé y practica el bien. Así vivirás en la tierra y te apacentarás de la fidelidad.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Deléitate también en Yavé, Y Él te dará los deseos de tu corazón.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Encomienda a Yavé tu camino, Confía en Él, Y Él hará.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Exhibirá tu justicia como la luz, Y tu derecho como el mediodía.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Guarda silencio ante Yavé, Y espéralo con paciencia. No te impacientes a causa del que prospera en su camino, A causa del hombre que maquina perversidades.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Deja la ira, desecha el enojo, No te excites de alguna manera a hacer el mal.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Porque los perversos serán cortados, Pero los que esperan en Yavé heredarán la tierra.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Pues dentro de poco el perverso no existirá. Examinarás con diligencia su lugar, y no estará allí.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Pero los mansos poseerán la tierra, Y se deleitarán con abundante paz.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Maquina el inicuo contra el justo, Y cruje sus dientes contra él.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
ʼAdonay se ríe de él, Porque ve que le llega su día.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Los impíos desenvainaron espada y tensaron su arco Para derribar al pobre y al menesteroso, Para matar a los rectos de conducta.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Su espada penetrará en su propio corazón, Y sus arcos serán quebrados.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Mejor es lo poco del justo, Que la abundancia de muchos perversos.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Porque los brazos de los perversos serán quebrados, Pero Yavé sostiene a los justos.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Yavé conoce los días de los íntegros, Y la heredad de ellos será eterna.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
No serán avergonzados en tiempo adverso, Y en días de hambre serán saciados.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Pero los perversos perecerán. Los enemigos de Yavé serán consumidos Como el verdor de los prados. Desvanecerán como el humo.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
El perverso toma prestado y no paga, Pero el justo es compasivo y da.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Porque los benditos por Él heredarán la tierra, Pero los malditos por Él serán cortados.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Por Yavé son establecidos los pasos del hombre En cuyo camino Él se deleita.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Aunque caiga, no quedará postrado, Porque Yavé sostiene su mano.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Fui joven, y ahora soy anciano, Y no he visto justo desamparado, Ni a su descendencia que mendigue pan.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
En todo tiempo tiene misericordia, y presta, Y sus descendientes son para bendición.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Apártate del mal y practica la rectitud, Y vivirás para siempre.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Porque Yavé ama la justicia, Y no desampara a sus piadosos. Para siempre son guardados sus santos, Pero la descendencia de los perversos será cortada.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Los justos heredarán la tierra, Y vivirán en ella para siempre.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
La boca del justo expresa sabiduría y habla justicia.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La Ley de su ʼElohim está en su corazón. Sus pasos no resbalan.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
El perverso acecha al justo Y trata de matarlo.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Yavé no lo dejará en su mano, Ni permitirá que sea condenado cuando sea juzgado.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Espera a Yavé y guarda tu camino. Él te exaltará para que poseas la tierra. Cuando los perversos sean cortados, Tú lo verás.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
He visto al perverso en gran poder Extenderse como árbol frondoso en su propio suelo.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Pero luego pasó y no fue más, Lo busqué, y no fue hallado.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Considera al hombre recto y mira al justo, Porque hay un final feliz para el hombre de paz.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Pero los transgresores serán destruidos por completo. La posteridad de los perversos será cortada.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
La salvación de los justos es de Yavé. Él es su Fortaleza en el tiempo de angustia.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Yavé los ayuda y los libra. Los liberta de los perversos y los salva, Porque se refugian en Él.

< Zabura 37 >