< Zabura 37 >
1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Por David. No te preocupes por los malhechores, ni tengáis envidia de los que obran con injusticia.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Porque pronto serán cortados como la hierba, y se marchitan como la hierba verde.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Confía en Yahvé y haz el bien. Habita en la tierra y disfruta de un pasto seguro.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Deléitate también en Yahvé, y te dará los deseos de tu corazón.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Encomienda tu camino a Yahvé. Confía también en él y lo hará:
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
hará que tu justicia brille como la luz, y tu justicia como el sol del mediodía.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Descansa en Yahvé y espéralo con paciencia. No te preocupes por el que prospera en su camino, por el hombre que hace que los complots malvados ocurran.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Deja de enojarte y abandona la ira. No te preocupes; eso sólo conduce a hacer el mal.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Porque los malhechores serán eliminados, pero los que esperan a Yahvé heredarán la tierra.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Todavía un poco de tiempo, y los malvados ya no existirán. Sí, aunque busques su lugar, no está allí.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Pero los humildes heredarán la tierra, y se deleitarán en la abundancia de la paz.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
El malvado conspira contra el justo, y le rechina los dientes.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
El Señor se reirá de él, porque ve que se acerca su día.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Los malvados han sacado la espada y han tensado su arco, para abatir a los pobres y necesitados, para matar a los que son rectos en el camino.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Su espada entrará en su propio corazón. Sus arcos se romperán.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Mejor es lo poco que tiene el justo, que la abundancia de muchos malvados.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Porque los brazos de los impíos serán quebrados, pero Yahvé sostiene a los justos.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Yahvé conoce los días de los perfectos. Su herencia será para siempre.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
No serán defraudados en el tiempo del mal. En los días de hambre serán satisfechos.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Pero los impíos perecerán. Los enemigos de Yahvé serán como la belleza de los campos. Desaparecerán... se desvanecen como el humo.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Los malvados piden prestado y no lo devuelven, pero los justos dan generosamente.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Porque los bendecidos por él heredarán la tierra. Los que sean maldecidos por él serán cortados.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Los pasos del hombre son establecidos por Yahvé. Se deleita en su camino.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Aunque tropiece, no caerá, porque Yahvé lo sostiene con su mano.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
He sido joven y ahora soy viejo, pero no he visto al justo abandonado, ni a sus hijos mendigando el pan.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Todo el día trata con gracia y presta. Su descendencia está bendecida.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Apártate del mal y haz el bien. Vive seguro para siempre.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Porque Yahvé ama la justicia, y no abandona a sus santos. Se conservan para siempre, pero los hijos de los malvados serán cortados.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Los justos heredarán la tierra, y vivir en ella para siempre.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
La boca del justo habla de sabiduría. Su lengua habla con justicia.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La ley de su Dios está en su corazón. Ninguno de sus pasos se deslizará.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Los malvados vigilan a los justos, y buscan matarlo.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
El Señor no lo dejará en sus manos, ni condenarlo cuando sea juzgado.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Esperen a Yahvé y guarden su camino, y te exaltará para que heredes la tierra. Cuando los malvados sean cortados, lo verás.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
He visto a los malvados con gran poder, extendiéndose como un árbol verde en su tierra natal.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Pero pasó, y he aquí que no estaba. Sí, lo busqué, pero no lo encontré.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Marca al hombre perfecto y ve al recto, porque hay un futuro para el hombre de paz.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
En cuanto a los transgresores, serán destruidos juntos. El futuro de los malvados será cortado.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Pero la salvación de los justos viene de Yahvé. Él es su baluarte en el tiempo de los problemas.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Yahvé los ayuda y los rescata. Los rescata de los malvados y los salva, porque se han refugiado en él.