< Zabura 37 >
1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
De David. No te acalores a causa de los malvados, ni envidies a los que cometen la iniquidad.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Porque muy pronto serán cortados, como el heno, y como hierba verde se secarán.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Tú, espera en Yahvé y obra el bien; permanece en la tierra y cultiva la rectitud.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Pon tus delicias en Yahvé, y Él te otorgará lo que tu corazón busca.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Entrega a Yahvé tu camino; confíate a Él y déjale obrar.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Él hará aparecer tu justicia como el día, y tu causa como la luz meridiana.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Calla ante Yahvé y espera de Él; no te acalores a causa del que prospera en su camino, del hombre que obra torcidamente.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Depón el rencor y aplaca la ira, no te irrites: pues sería peor;
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
porque los que obran mal serán exterminados, mas los que esperan en Yahvé heredarán la tierra.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Aguarda un poco, y el impío ya no estará; y si buscas su lugar, no lo hallarás.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
En tanto que los mansos poseerán la tierra, y se deleitarán en abundancia de paz.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
El impío urde males contra el justo, y a su vista rechina los dientes;
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
pero Yahvé se ríe de él, porque está viendo llegar su día.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Los perversos desenvainan la espada y tienden su arco, para derribar al afligido y al desvalido, y trucidar a los que son rectos.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Pero la espada se les clavará en su propio corazón, y sus arcos se romperán.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Más vale lo poco del justo que la gran opulencia de los pecadores;
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
porque serán quebrados los brazos de los impíos, en tanto que a los justos los sostiene Yahvé.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Lleva cuenta Yahvé de los días de los justos, y su herencia será eterna.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
No se verán confundidos en tiempo de calamidad, y en los días de hambre serán saciados.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Mas los impíos perecerán; y los enemigos de Yahvé, los altivos ensoberbecidos en su corazón, se desvanecerán como el humo.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
El malvado toma en préstamo y no devuelve, mas el justo es compasivo y da;
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
porque los benditos poseerán la tierra, pero los malditos serán exterminados.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Yahvé dirige los pasos del hombre, al que le agrada Él le afirma el camino.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Aunque resbalare, no caerá postrado, porque Yahvé lo sostiene con su mano.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Joven fui y ahora soy viejo, mas nunca he visto al justo desamparado, ni a sus hijos mendigando el pan.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
En todo tiempo es misericordioso y presta, y su estirpe es bendecida.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Huye tu del mal y haz el bien, y habitarás por siempre.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Pues Yahvé ama la justicia, y no abandona a sus santos; los impíos serán exterminados, y su descendencia perecerá.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Los justos poseerán la tierra, y habitarán en ella para siempre.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
La boca del justo profiere sabiduría, y su lengua habla con rectitud.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La Ley de su Dios está en su corazón, y sus pasos no vacilan.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
El impío anda en acecho del justo, y busca cómo quitarle la vida;
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
pero Yahvé no lo deja en sus manos, ni permite que le condenen cuando es juzgado.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Cuenta con Yahvé y sigue su camino; Él te conducirá a la herencia de la tierra; asistirás gozoso al exterminio de los perversos.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
Vi al impío sumamente empinado y expandiéndose, como un cedro del Líbano;
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
pasé de nuevo, y ya no estaba; lo busqué, y no fue encontrado.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Observa al hombre íntegro y mira al que es recto, porque el hombre pacífico tendrá porvenir,
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
en tanto que los rebeldes todos perecerán, y la posteridad de los impíos será extirpada.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
De Yahvé viene la salvación de los justos; Él es su fortaleza en los días aciagos.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Yahvé les da ayuda y libertad; los saca de las manos de los impíos y los salva, porque a Él se acogieron.