< Zabura 37 >
1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Dāvida dziesma. Neapskaities par bezdievīgiem, neiekarsies par ļauna darītājiem,
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Jo tā kā zāle tie drīz top nocirsti, un savītīs kā zaļa zāle.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Cerē uz To Kungu un dari labu, paliec savā zemē un uzturies ar uzticību.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Priecājies iekš Tā Kunga, tad Viņš tev dos tavas sirds lūgšanas.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Pavēli Tam Kungam savu ceļu un cerē uz Viņu, tad Viņš gan darīs.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Viņš liks aust tavai taisnībai kā gaismai un tavai tiesai kā dienas spožumam.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Ciet klusu Tam Kungam un gaidi uz Viņu, neapskaities par to, kam ceļš labi izdodas, par vīru, kas dodas uz blēdīgiem padomiem.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Atstājies no dusmības un mities no bardzības, nesaskaities, ka tu ļauna nedari.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Jo ļaunie taps izdeldēti; bet kas uz To Kungu gaida, tie zemi iemantos.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Mazs brīdis vēl, un bezdievīgā vairs nav; un kad Tu raudzīsi pēc viņa vietas, tad tā vairs nav.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Bet lēnprātīgie iemantos zemi un priecāsies lielā mierā.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Bezdievīgais glūn uz taisno un sakož savus zobus pret viņu.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
Bet Tas Kungs par viņu smejas, jo tas redz, ka viņa diena nāks.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Bezdievīgie izvelk zobenu un uzvelk savu stopu, gāzt bēdīgo un nabagu un nokaut tos, kas uz taisniem ceļiem.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Bet viņu zobens ies viņu pašu sirdī, un viņu stopi taps salauzti.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Tas mazums, kas taisnam, ir labāks, nekā tā bagātība, kas daudz bezdievīgiem.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Jo bezdievīgiem elkonis taps salauzts, bet Tas Kungs uztur taisnos.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Tas Kungs zina sirds skaidro dienas, un viņu manta paliks mūžīgi.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Bēdu laikā tie netaps kaunā, un bada laikā tie taps paēdināti.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Jo bezdievīgie ies bojā, un Tā Kunga ienaidnieki kā lauku jaukums iznīks, tie iznīks kā dūmi.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Bezdievīgais aizņem uz parādu un neatdod, bet taisnais ir žēlīgs un devīgs.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Jo Tā Kunga svētītie iemantos zemi, bet Viņa nolādētie taps izdeldēti.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
No Tā Kunga būs stiprināti tāda vīra soļi, un ved tādu, kura ceļš viņam patīk.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Ja viņš krīt, tad nepaliek guļam, jo Tas Kungs viņu tur pie rokas.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Es esmu jauns bijis un arī vecs palicis, bet es neesmu redzējis taisno atstātu, nedz viņa dzimumu meklējam maizi.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Vienmēr viņš apžēlojās un aizdod, un viņa dzimums ir par svētību.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Atstājies no ļauna un dari labu, tad tu paliksi mūžīgi.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Jo Tas Kungs mīl tiesu un neatstās Savus svētos; tie top mūžīgi pasargāti, bet bezdievīgo dzimums top izdeldēts.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Taisnie iemantos zemi, un dzīvos iekš tās mūžam.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
Taisnā mute izteic gudrību, un viņa mēle runā tiesu.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
Dieva bauslība ir viņa sirdī, viņa soļi nestraipelēs.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Bezdievīgais glūn uz taisno un meklē viņu nokaut.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Bet Tas Kungs to nepamet viņa rokā, un to nepazudina, kad to tiesā.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Gaidi uz To Kungu un sargi Viņa ceļu, tad Viņš tevi paaugstinās, ka tu zemi iemanto; tu redzēsi, ka bezdievīgie taps izdeldēti.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
Es esmu redzējis vienu bezdievīgu, tas darīja varas darbus un zaļoja kā paša audzis koks.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Bet tas iznīka, un redzi, tā nebija vairs; es pēc viņa vaicāju bet viņš netapa atrasts.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Ņem vērā sirds skaidro un uzlūko taisno, jo tādam vīram beidzot labi klāsies.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Bet pārkāpēji kopā taps samaitāti, bezdievīgie taps beidzot izdeldēti.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Bet taisno palīdzība ir no Tā Kunga; Tas tiem ir par stiprumu bēdu laikā.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Un Tas Kungs tiem palīdzēs un tos izglābs, Viņš tos izglābs no bezdievīgiem, un tos izpestīs, jo tie paļaujas uz Viņu.