< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Di Davide. Non ti crucciare a cagion de’ malvagi; non portare invidia a quelli che operano perversamente;
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
perché saran di subito falciati come il fieno, e appassiranno come l’erba verde.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Confidati nell’Eterno e fa’ il bene; abita il paese e coltiva la fedeltà.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Prendi il tuo diletto nell’Eterno, ed egli ti darà quel che il tuo cuore domanda.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Rimetti la tua sorte nell’Eterno; confidati in lui, ed egli opererà
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Egli farà risplendere la tua giustizia come la luce, e il tuo diritto come il mezzodì.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Sta’ in silenzio dinanzi all’Eterno, e aspettalo; non ti crucciare per colui che prospera nella sua via, per l’uomo che riesce ne’ suoi malvagi disegni.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Cessa dall’ira e lascia lo sdegno; non crucciarti; ciò non conduce che al mal fare.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Poiché i malvagi saranno sterminati; ma quelli che sperano nell’Eterno possederanno la terra.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Ancora un poco e l’empio non sarà più; tu osserverai il suo luogo, ed egli non vi sarà più.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Ma i mansueti erederanno la terra e godranno abbondanza di pace.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
L’empio macchina contro il giusto e digrigna i denti contro lui.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
Il Signore si ride di lui, perché vede che il suo giorno viene.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Gli empi han tratto la spada e teso il loro arco per abbattere il misero e il bisognoso, per sgozzare quelli che vanno per la via diritta.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
La loro spada entrerà loro nel cuore, e gli archi loro saranno rotti.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Meglio vale il poco del giusto che l’abbondanza di molti empi.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Perché le braccia degli empi saranno rotte; ma l’Eterno sostiene i giusti.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
L’Eterno conosce i giorni degli uomini integri; e la loro eredità durerà in perpetuo.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Essi non saran confusi nel tempo dell’avversità, e saranno saziati nel tempo dalla fame.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Ma gli empi periranno; e i nemici dell’Eterno, come grasso d’agnelli, saran consumati e andranno in fumo.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
L’empio prende a prestito e non rende; ma il giusto è pietoso e dona.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Poiché quelli che Dio benedice erederanno la terra, ma quelli ch’ei maledice saranno sterminati.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
I passi dell’uomo dabbene son diretti dall’Eterno ed egli gradisce le vie di lui.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Se cade, non è però atterrato, perché l’Eterno lo sostiene per la mano.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Io sono stato giovane e son anche divenuto vecchio, ma non ho visto il giusto abbandonato, né la sua progenie accattare il pane.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Egli tutti i giorni è pietoso e presta, e la sua progenie è in benedizione.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Ritraiti dal male e fa’ il bene, e dimorerai nel paese in perpetuo.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Poiché l’Eterno ama la giustizia e non abbandona i suoi santi; essi son conservati in perpetuo; ma la progenie degli empi sarà sterminata.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
I giusti erederanno la terra e l’abiteranno in perpetuo.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
La bocca del giusto proferisce sapienza e la sua lingua pronunzia giustizia.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La legge del suo Dio è nel suo cuore; i suoi passi non vacilleranno.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
L’empio spia il giusto e cerca di farlo morire.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
L’Eterno non l’abbandonerà nelle sue mani, e non lo condannerà quando verrà in giudicio.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Aspetta l’Eterno e osserva la sua via; egli t’innalzerà perché tu eredi la terra; e quando gli empi saranno sterminati, tu lo vedrai.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
Io ho veduto l’empio potente, e distendersi come albero verde sul suolo natìo;
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
ma è passato via, ed ecco, non è più; io l’ho cercato, ma non s’è più trovato.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Osserva l’uomo integro e considera l’uomo retto; perché v’è una posterità per l’uomo di pace.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Mentre i trasgressori saranno tutti quanti distrutti; la posterità degli empi sarà sterminata.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Ma la salvezza dei giusti procede dall’Eterno; egli è la loro fortezza nel tempo della distretta.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
L’Eterno li aiuta e li libera: li libera dagli empi e li salva, perché si sono rifugiati in lui.

< Zabura 37 >