< Zabura 37 >
1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Von David. Erzürne dich nicht über die Bösen, und sei nicht neidisch auf die Übeltäter!
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Denn sie werden schnell verdorren wie das Gras und verwelken wie das grüne Kraut.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Vertraue auf den HERRN und tue Gutes, wohne im Lande und übe Treue;
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
und habe deine Lust an dem HERRN, so wird er dir geben, was dein Herz begehrt!
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Befiehl dem HERRN deinen Weg und vertraue auf ihn, so wird er handeln
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
und wird deine Gerechtigkeit an den Tag bringen wie das Licht und dein Recht wie den Mittag.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Halte still dem HERRN und warte auf ihn; erzürne dich nicht über den, welchem sein Weg gelingt, über den Mann, der Ränke übt!
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Stehe ab vom Zorn und laß den Grimm; erzürne dich nicht! Es entsteht nur Böses daraus.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Denn die Übeltäter werden ausgerottet; die aber auf den HERRN warten, werden das Land ererben.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Nur noch ein Weilchen, so wird der Gottlose nicht mehr sein, und wenn du dich nach seiner Wohnung erkundigst, so ist er nicht mehr da!
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Aber die Sanftmütigen werden das Land ererben und sich großen Friedens erfreuen.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Der Gottlose macht Anschläge wider den Gerechten und knirscht mit den Zähnen über ihn;
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
aber mein Herr lacht seiner; denn er hat dafür gesorgt, daß sein Tag kommt!
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Die Gottlosen haben das Schwert gezückt und ihren Bogen gespannt, um den Elenden und Armen zu fällen und die umzubringen, deren Weg richtig ist.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Ihr Schwert wird in ihr eigenes Herz dringen, und ihr Bogen wird zerbrochen werden!
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Das Wenige, das ein Gerechter hat, ist besser als der Überfluß vieler Gottlosen.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Denn die Arme der Gottlosen werden zerbrochen; aber die Gerechten unterstützt der HERR.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Der HERR kennt die Tage der Frommen, und ihr Erbe wird ewiglich bestehen.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Sie sollen nicht zuschanden werden zur bösen Zeit, sondern genug haben auch in den Tagen der Hungersnot;
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
aber die Gottlosen werden umkommen und die Feinde des HERRN dahinschwinden wie die Pracht der Auen; wie Rauch verschwinden sie.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Der Gottlose borgt und zahlt nicht zurück; der Gerechte aber ist barmherzig und gibt.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Denn die [vom HERRN] Gesegneten werden das Land ererben, aber seine Verfluchten sollen ausgerottet werden.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Vom HERRN werden die Schritte des Mannes bestätigt, wenn ihm sein Weg gefällt.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Fällt er, so wird er nicht weggeworfen; denn der HERR stützt seine Hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Ich bin jung gewesen und alt geworden und habe nie den Gerechten verlassen gesehen, oder seinen Samen um Brot betteln.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Er ist allezeit barmherzig und leiht gern, und sein Same wird zum Segen.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Weiche vom Bösen und tue Gutes, so wirst du ewiglich bleiben!
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Denn der HERR hat das Recht lieb und verläßt seine Frommen nicht; sie werden ewiglich bewahrt, aber der Same der Gottlosen wird ausgerottet.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Die Gerechten werden das Land ererben und für immer darin wohnen.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
Des Gerechten Mund tut Weisheit kund, und seine Zunge redet recht.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
Das Gesetz seines Gottes ist in seinem Herzen, und seine Schritte wanken nicht.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Der Gottlose lauert auf den Gerechten und sucht ihn zu töten.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Aber der HERR wird ihn nicht seiner Hand überlassen und läßt ihn nicht verdammen, wenn er gerichtet wird.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Harre des HERRN und bewahre seinen Weg, so wird er dich erhöhen, daß du das Land ererbest und die Ausrottung der Gottlosen sehest!
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
Ich sah einen Gottlosen, der war trotzig und breitete sich aus wie ein grünender, wilder Baum.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Aber als man wieder vorbeiging, da war er nicht mehr; ich suchte ihn, aber man fand ihn nicht.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Achte auf den Unschuldigen und siehe auf den Redlichen; dem Mann des Friedens wird eine Zukunft zuteil!
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Aber die Übertreter werden allesamt vertilgt, und der Nachwuchs der Gottlosen wird ausgerottet.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Aber das Heil der Gerechten kommt vom HERRN; er ist ihre Zuflucht zur Zeit der Not.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Der HERR wird ihnen beistehen und sie erretten, er wird sie erretten von den Gottlosen und ihnen Heil verschaffen; denn sie bergen sich bei ihm.