< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Von David. Entrüste dich nicht über die Bösen
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
denn schnell wie das Gras verwelken sie und verdorren wie grünender Rasen.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Vertrau auf den HERRN und tu das Gute, bleib wohnen im Lande und übe Redlichkeit
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
und habe deine Lust am HERRN: so wird er dir geben, was dein Herz begehrt.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Befiehl dem HERRN deine Wege und vertraue auf ihn: er wird’s wohl machen
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
und deine Gerechtigkeit strahlen lassen wie das Licht und dein Recht wie den hellen Mittag.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Sei stille dem HERRN und harre auf ihn, entrüste dich nicht über den, der Glück hat bei seinem Tun, über den Mann, der Ränke übt!
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Steh ab vom Zorn und entsage dem Grimm, entrüste dich nicht: es führt nur zum Bösestun!
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Denn die Übeltäter werden ausgerottet, doch die da harren des HERRN, die werden das Land besitzen.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Nur noch ein Weilchen, so wird der Frevler nicht mehr sein, und siehst du dich um nach seiner Stätte, so ist er nicht mehr da;
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
die stillen Dulder aber werden das Land besitzen und sich freun an der Fülle des Friedens.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Böses sinnt der Frevler gegen den Gerechten und knirscht mit den Zähnen gegen ihn;
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
der Allherr aber lacht über ihn, denn er sieht, daß sein Tag kommt.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Die Frevler zücken das Schwert und spannen den Bogen, um den Dulder und Armen niederzustrecken und die redlich Wandelnden hinzumorden;
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
doch ihr Schwert dringt ihnen ins eigne Herz, und ihre Bogen werden zerbrochen.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Das geringe Gut des Gerechten ist besser als der Überfluß vieler Gottlosen;
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
denn die Arme der Gottlosen werden zerbrochen, die Gerechten aber stützt der HERR.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Der HERR kennt wohl die Tage der Frommen, und ihr Besitz ist für immer gesichert;
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
sie werden nicht zuschanden in böser Zeit, nein, in den Tagen des Hungers werden sie satt.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Dagegen die Gottlosen gehen zugrunde, und die Feinde des HERRN sind wie die Pracht der Auen: sie vergehen wie Rauch, sie vergehen!
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Der Gottlose muß borgen und kann nicht zahlen, der Gerechte aber schenkt und gibt;
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
denn die vom HERRN Gesegneten erben das Land, aber die von ihm Verfluchten werden vernichtet.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Vom HERRN her werden die Schritte des Mannes gefestigt, und zwar wenn Gefallen er hat an seinem Wandel;
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
wenn er strauchelt, stürzt er nicht völlig nieder, denn der HERR stützt ihm die Hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Ich bin jung gewesen und alt geworden, doch hab’ ich nie den Gerechten verlassen gesehn, noch seine Kinder betteln um Brot.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Allzeit kann er schenken und darleihn, und auch noch seine Kinder sind zum Segen.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Halte dich fern vom Bösen und tu das Gute, so wirst du für immer wohnen bleiben;
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Denn der HERR hat das Recht lieb und verläßt seine Frommen nicht: ewiglich werden sie behütet, doch der Gottlosen Nachwuchs wird ausgerottet.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Die Gerechten werden das Land besitzen und bleiben in ihm wohnen für immer.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
Des Gerechten Mund läßt Weisheit hören, und seine Zunge redet Recht;
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
das Gesetz seines Gottes wohnt ihm im Herzen, und seine Schritte wanken nicht.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Der Gottlose lauert dem Gerechten auf und sucht ihn ums Leben zu bringen;
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
doch der HERR läßt ihn nicht fallen in seine Hand und läßt ihn nicht verdammen vor Gericht.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Harre des HERRN und halte dich an seinen Weg, so wird er dich erhöhn zum Besitz des Landes; an der Gottlosen Vernichtung wirst du deine Freude sehn.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
Ich hab’ einen Frevler gesehen, der trat gar trotzig auf und spreizte sich stolz wie ein grünender, ragender Baum;
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
doch als ich (wieder) vorüberging, da war er verschwunden, und als ich ihn suchte, war er nicht mehr zu finden.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Bleibe (also) fromm und halte dich recht, denn solchen wird es zuletzt wohl ergehn;
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
die Frevler aber werden allesamt vertilgt, und der Gottlosen Nachwuchs wird ausgerottet.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Die Hilfe der Gerechten kommt vom HERRN: er ist ihre Schutzwehr zur Zeit der Not;
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
denn der HERR steht ihnen bei und rettet sie; er rettet sie von den Frevlern und bringt ihnen Hilfe, weil auf ihn sie ihr Vertrauen setzen.

< Zabura 37 >