< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Ein Psalm Davids. Erzürne dich nicht über die Bösen; sei nicht neidisch über die Übeltäter!
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Denn wie das Gras werden sie bald abgehauen und wie das grüne Kraut werden sie verwelken.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Hoffe auf den HERRN und tue Gutes; bleibe im Lande und nähre dich redlich.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Habe deine Lust am HERRN; der wird dir geben, was dein Herz wünschet.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Befiehl dem HERRN deine Wege und hoffe auf ihn; er wird's wohl machen
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
und wird deine Gerechtigkeit hervor bringen wie das Licht und dein Recht wie den Mittag.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Sei stille dem HERRN und warte auf ihn! Erzürne dich nicht über den, dem sein Mutwille glücklich fortgehet.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Stehe ab vom Zorn und laß den Grimm; erzürne dich nicht, daß du auch übel tust.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Denn die Bösen werden ausgerottet; die aber des HERRN harren, werden das Land erben.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Es ist noch um ein kleines, so ist der Gottlose nimmer; und wenn du nach seiner Stätte sehen wirst, wird er weg sein.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Aber die Elenden werden das Land erben und Lust haben in großem Frieden.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Der Gottlose dräuet dem Gerechten und beißet seine Zähne zusammen über ihn.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
Aber der HERR lachet sein; denn er siehet, daß sein Tag kommt.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Die Gottlosen ziehen das Schwert aus und spannen ihren Bogen, daß sie fällen den Elenden und Armen und schlachten die Frommen.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Aber ihr Schwert wird in ihr Herz gehen, und ihr Bogen wird zerbrechen.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Das Wenige, das ein Gerechter hat, ist besser denn das große Gut vieler Gottlosen.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Denn der Gottlosen Arm wird zerbrechen; aber der HERR erhält die Gerechten.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Der HERR kennet die Tage der Frommen, und ihr Gut wird ewiglich bleiben.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Sie werden nicht zuschanden in der bösen Zeit, und in der Teurung werden sie genug haben.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Denn die Gottlosen werden umkommen, und die Feinde des HERRN, wenn sie gleich sind wie eine köstliche Aue, werden sie doch vergehen, wie der Rauch vergehet.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Der Gottlose borget und bezahlet nicht; der Gerechte aber ist barmherzig und milde.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Denn seine Gesegneten erben das Land; aber seine Verfluchten werden ausgerottet.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Von dem HERRN wird solches Mannes Gang gefördert und hat Lust an seinem Wege.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Fällt er, so wird er nicht weggeworfen; denn der HERR erhält ihn bei der Hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Ich bin jung gewesen und alt worden und habe noch nie gesehen den Gerechten verlassen oder seinen Samen nach Brot gehen.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Er ist allezeit barmherzig und leihet gerne; und sein Same wird gesegnet sein.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Laß vom Bösen und tue Gutes, und bleibe immerdar.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Denn der HERR hat das Recht lieb und verläßt seine Heiligen nicht; ewiglich werden sie bewahret; aber der Gottlosen Same wird ausgerottet.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Die Gerechten erben das Land und bleiben ewiglich drinnen.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
Der Mund des Gerechten redet die Weisheit, und seine Zunge lehret das Recht.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
Das Gesetz seines Gottes ist, in seinem Herzen, seine Tritte gleiten nicht.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Der Gottlose lauert auf den Gerechten und gedenkt ihn zu töten.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Aber der HERR läßt ihn nicht in seinen Händen und verdammt ihn nicht, wenn er verurteilt wird.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Harre auf den HERRN und halte seiner Weg, so wird er dich erhöhen, daß du das Land erbest; du wirst's sehen, daß die Gottlosen ausgerottet werden.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
Ich habe gesehen einen Gottlosen, der war trotzig und breitete sich aus und grünete wie ein Lorbeerbaum.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Da man vorüberging, siehe, da war er dahin; ich fragte nach ihm, da ward er nirgend funden.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Bleibe fromm und halte dich recht, denn solchem wird's zuletzt wohlgehen.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Die Übertreter aber werden vertilget miteinander, und die Gottlosen werden zuletzt ausgerottet.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Aber der HERR hilft den Gerechten; der ist ihre Stärke in der Not.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Und der HERR wird ihnen beistehen und wird sie erretten; er wird sie von den Gottlosen erretten und ihnen helfen; denn sie trauen auf ihn.

< Zabura 37 >