< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Psaume de David. [Aleph.] Ne te dépite point à cause des méchants, ne sois point jaloux de ceux qui s'adonnent à la perversité.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Car ils seront soudainement retranchés comme le foin, et se faneront comme l'herbe verte.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
[Beth.] Assure-toi en l'Eternel, et fais ce qui est bon; habite la terre, et te nourris de vérité.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Et prends ton plaisir en l'Eternel, et il t'accordera les demandes de ton cœur.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
[Guimel.] Remets ta voie sur l'Eternel, et te confie en lui; et il agira;
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Et il manifestera ta justice comme la clarté, et ton droit comme le midi.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
[Daleth.] Demeure tranquille te confiant en l'Eternel, et l'attends; ne te dépite point à cause de celui qui fait bien ses affaires, à cause, [dis-je], de l'homme qui vient à bout de ses entreprises.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
[He.] Garde-toi de te courroucer, et renonce à la colère; ne te dépite point, au moins pour mal faire.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Car les méchants seront retranchés; mais ceux qui se confient en l'Eternel hériteront la terre.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
[Vau.] Encore donc un peu de temps, et le méchant ne sera plus; et tu prendras garde à son lieu, et il n'y sera plus.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Mais les débonnaires hériteront la terre, et jouiront à leur aise d'une grande prospérité.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
[Zain.] Le méchant machine contre le juste, et grince ses dents contre lui.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
Le Seigneur se rira de lui, car il a vu que son jour approche.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
[Heth.] Les méchants ont tiré leur épée, et ont bandé leur arc, pour abattre l'affligé, et le pauvre, [et] pour massacrer ceux qui marchent dans la droiture.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
[Mais] leur épée entrera dans leur cœur, et leurs arcs seront rompus.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
[Teth.] Mieux vaut au juste le peu qu'il a, que l'abondance à beaucoup de méchants.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Car les bras des méchants seront cassés, mais l'Eternel soutient les justes.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
[Jod.] L'Eternel connaît les jours de ceux qui sont intègres, et leur héritage demeurera à toujours.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Ils ne seront point confus au mauvais temps, mais ils seront rassasiés au temps de la famine.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
[Caph.] Mais les méchants périront, et les ennemis de l'Eternel s'évanouiront comme la graisse des agneaux, ils s'en iront en fumée.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
[Lamed.] Le méchant emprunte, et ne rend point; mais le juste a compassion, et donne.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Car les bénis [de l'Eternel] hériteront la terre; mais ceux qu'il a maudits seront retranchés.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
[Mem.] Les pas de l'homme [qu'il a béni] sont conduits par l'Eternel, et il prend plaisir à ses voies.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
S'il tombe, il ne sera pas [entièrement] abattu; car l'Eternel lui soutient la main.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
[Nun.] J'ai été jeune, et j'ai atteint la vieillesse, mais je n'ai point vu le juste abandonné, ni sa postérité mendiant son pain.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Il est ému de pitié tout le jour, et il prête; et sa postérité est en bénédiction.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
[Samech.] Retire-toi du mal, et fais le bien; et tu auras une demeure éternelle.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Car l'Eternel aime ce qui est juste, et il n'abandonne point ses bien-aimés; c'est pourquoi ils sont gardés à toujours; mais la postérité des méchants est retranchée.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
[Hajin.] Les justes hériteront la terre, et y habiteront à perpétuité.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
[Pe.] La bouche du juste proférera la sagesse, et sa langue prononcera la justice.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La Loi de son Dieu est dans son cœur, aucun de ses pas ne chancellera.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
[Tsade.] Le méchant épie le juste, et cherche à le faire mourir.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
L'Eternel ne l'abandonnera point entre ses mains, et ne le laissera point condamner quand on le jugera.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
[Koph.] Attends l'Eternel, et prends garde à sa voie, et il t'exaltera, afin que tu hérites la terre, [et] tu verras comment les méchants seront retranchés.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
[Res.] J'ai vu le méchant terrible, et s'étendant comme un laurier vert;
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Mais il est passé, et voilà, il n'est plus; je l'ai cherché, et il ne s'est point trouvé.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
[Scin.] Prends garde à l'homme intègre, et considère l'homme droit; car la fin d'un tel homme est la prospérité.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Mais les prévaricateurs seront tous ensemble détruits, et ce qui sera resté des méchants sera retranché.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
[Thau.] Mais la délivrance des justes [viendra] de l'Eternel, il sera leur force au temps de la détresse.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Car l'Eternel leur aide, et les délivre: il les délivrera des méchants, et les sauvera, parce qu'ils se seront confiés en lui.

< Zabura 37 >