< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
De David. Ne cherche pas à imiter les méchants; ne porte pas envie à ceux qui font le mal.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Car, comme l'herbe des champs, ils seront bientôt flétris; comme la plante verte, ils ne tarderont pas à tomber.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Espère au Seigneur et fais le bien; habite la terre, et tu seras nourri de ses richesses.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Délecte-toi dans le Seigneur, et il t'accordera ce que ton cœur aura demandé.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Révèle au Seigneur ta voie; espère en lui, et il agira.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Il manifestera ta justice comme une lumière, et ton jugement comme le midi.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Soumets-toi au Seigneur, et prie-le; ne porte pas envie à celui qui prospère dans sa voie, à l'homme qui commet des injustices.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Calme ta colère, laisse tomber ton courroux; ne cherche pas à devenir méchant;
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Car les méchants seront exterminés; mais ceux qui attendent le Seigneur auront la terre pour héritage.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Encore un peu de temps, et le pécheur ne sera plus; tu chercheras sa place, et tu ne la trouveras point.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Mais les doux auront la terre pour héritage, et ils se délecteront dans la plénitude de la paix.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Le pécheur épiera le juste, et il grincera des dents contre lui.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
Et le Seigneur se rira de lui; car il voit que son jour approche.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Les pécheurs ont tiré l'épée; ils ont tendu leur arc pour abattre le pauvre et l'indigent, pour tuer ceux qui ont le cœur droit.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Que leur glaive s'enfonce dans leur propre cœur, et que leur arc soit brisé!
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Mieux vaut la pauvreté du juste que les grandes richesses des pécheurs;
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Car les bras des pécheurs seront broyés, et le Seigneur affermit les justes.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Le Seigneur connaît les voies des innocents, et leur héritage sera éternel.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Dans les temps de détresse, ils ne seront point confondus, et aux jours de famine ils seront rassasiés.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Mais les pécheurs périront, et les ennemis de Dieu sont à peine parvenus aux honneurs et à la gloire qu'ils s'évanouissent comme une fumée qui se disperse.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Le pécheur emprunte, et il ne rendra pas; le juste a compassion, et il donne.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Ceux qui bénissent le Seigneur auront la terre pour héritage; ceux qui le maudissent seront exterminés.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Les pas de l'homme sont conduits par le Seigneur, qui se complaira dans sa voie.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
S'il tombe, il ne se brisera point; car le Seigneur le soutient de sa main.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
J'ai été jeune et je suis devenu vieux, et je n'ai point vu le juste délaissé, ni ses enfants demander leur pain.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Il est compatissant, et chaque jour il prête, et sa race sera bénie.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Détourne-toi du mal et fais le bien, et habite la terre dans les siècles des siècles.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Car le Seigneur aime la justice, et il n'abandonnera jamais ses saints; il les prendra sous garde éternellement; les innocents seront vengés, et la race des impies sera détruite.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Les justes auront la terre pour héritage, et ils l'habiteront durant les siècles des siècles.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
La bouche du juste méditera la sagesse, et sa langue parlera la justice.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La loi de son Dieu est dans son cœur, et ses pas ne seront jamais chancelants.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Le pécheur épie le juste; il cherche à le faire périr.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Mais le Seigneur ne le laissera pas en ses mains, et il ne le condamnera pas lorsqu'il sera jugé par le pécheur.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Attends le Seigneur et garde sa voie, et il t'élèvera pour que tu hérites de la terre; et lorsque les pécheurs auront péri, tu verras!
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
J'ai vu l'impie fier, exalté et élevé comme les cèdres du Liban:
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
J'ai passé et voilà qu'il n'était plus; et je l'ai cherché, et sa place n'a point été retrouvée.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Garde l'innocence, aie en vue la droiture; car il a une attente l'homme pacifique.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Mais les pervers seront exterminés tous à la fois; le résidu des impies sera exerminé.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Le salut des justes vient du Seigneur; il est leur appui au temps de l'affliction,
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Et le Seigneur les soutiendra, et il les délivrera, et il les ravira aux pécheurs, et il les sauvera, parce qu'ils ont espéré en lui.

< Zabura 37 >