< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
Par David. Ne t'inquiète pas à cause des méchants, et ne soyez pas jaloux de ceux qui travaillent dans l'injustice.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
Car ils seront bientôt fauchés comme l'herbe, et se flétrir comme l'herbe verte.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Ayez confiance en Yahvé, et faites le bien. Habitez le pays, et jouissez d'un pâturage sûr.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Fais aussi tes délices de Yahvé, et il te donnera les désirs de ton cœur.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Confie ton chemin à Yahvé. Ayez aussi confiance en lui, et il fera cela:
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
il fera briller ta justice comme la lumière, et ta justice comme le soleil de midi.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Reposez-vous en Yahvé, et attendez-le avec patience. Ne t'inquiète pas à cause de celui qui prospère dans sa voie, à cause de l'homme qui fait des complots méchants.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Cessez la colère, abandonnez la fureur. Ne vous inquiétez pas, cela ne mène qu'au mal.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Car les méchants seront exterminés, mais ceux qui espèrent en Yahvé hériteront du pays.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Encore un peu de temps, et les méchants ne seront plus. Oui, bien que vous cherchiez sa place, il n'y est pas.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
Mais les humbles hériteront du pays, et se délecteront dans l'abondance de la paix.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Le méchant complote contre le juste, et le fait grincer des dents.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
Le Seigneur se moquera de lui, car il voit que son jour arrive.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
Les méchants ont tiré l'épée, et ils ont bandé leur arc, pour rabaisser les pauvres et les nécessiteux, pour tuer ceux qui sont droits sur le chemin.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Leur épée entrera dans leur propre cœur. Leurs arcs seront brisés.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Mieux vaut un peu de ce que possède le juste, que l'abondance de beaucoup de méchants.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Car les bras des méchants seront brisés, mais Yahvé soutient les justes.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Yahvé connaît les jours des parfaits. Leur héritage sera éternel.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
Ils ne seront pas déçus au temps du malheur. Aux jours de famine, ils seront rassasiés.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Mais les méchants périront. Les ennemis de Yahvé seront comme la beauté des champs. Ils vont disparaître. disparaissent comme de la fumée.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
Les méchants empruntent et ne remboursent pas, mais les justes donnent généreusement.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Car ceux qui sont bénis par lui hériteront du pays. Ceux qui sont maudits par lui seront retranchés.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
Les pas de l'homme sont établis par Yahvé. Il se complaît dans sa voie.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
S'il trébuche, il ne tombera pas, car Yahvé le retient de sa main.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
J'ai été jeune, et maintenant je suis vieux, mais je n'ai pas vu les justes abandonnés, ni ses enfants mendiant pour du pain.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
Tout le jour, il traite avec bonté, il prête. Sa descendance est bénie.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Éloigne-toi du mal et fais le bien. Vivre en sécurité pour toujours.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
Car Yahvé aime la justice, et n'abandonne pas ses saints. Ils sont préservés pour toujours, mais les enfants des méchants seront exterminés.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
Les justes hériteront du pays, et y vivre pour toujours.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
La bouche des justes parle de sagesse. Sa langue parle de justice.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
La loi de son Dieu est dans son cœur. Aucun de ses pas ne doit glisser.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
Les méchants surveillent les justes, et cherchent à le tuer.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
L'Éternel ne le laissera pas entre ses mains, ni le condamner lorsqu'il sera jugé.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Attendez Yahvé, et gardez sa voie, et il vous élèvera pour hériter du pays. Quand les méchants seront exterminés, vous le verrez.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
J'ai vu les méchants dans une grande puissance, se répandant comme un arbre vert dans son sol natal.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Mais il passa, et voici, il n'était plus. Oui, je l'ai cherché, mais il était introuvable.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Marquez l'homme parfait, et voyez le droit, car il y a un avenir pour l'homme de paix.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Quant aux transgresseurs, ils seront détruits ensemble. L'avenir des méchants sera coupé.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Mais le salut des justes vient de l'Éternel. Il est leur forteresse dans le temps de la détresse.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Yahvé leur vient en aide et les sauve. Il les délivre des méchants et les sauve, parce qu'ils se sont réfugiés en lui.

< Zabura 37 >