< Zabura 37 >
1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
A psalm of David. Do not be irritated because of evildoers; do not be envious of those who act unrighteously.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
For they will soon dry up as the grass and wither as the green plants.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Trust in Yahweh and do what is good; settle in the land and graze in faithfulness.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Then delight yourself in Yahweh, and he will give you the desires of your heart.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Give your ways to Yahweh; trust in him, and he will act on your behalf.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
He will display your justice like the daylight and your innocence like the day at noon.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Be still before Yahweh and wait patiently for him. Do not be angry if someone succeeds in what he does, or when he makes evil plots.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Do not be angry and frustrated. Do not worry. This only makes trouble.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
Evildoers will be cut off, but those who wait for Yahweh will inherit the land.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
In a little while the evil man will disappear; you will look at his place, but he will be gone.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
But the meek will inherit the land and will delight in great prosperity.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
The wicked man plots against the righteous and he grinds his teeth in rage against him.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
The Lord laughs at him, for he sees that his day is coming.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
The wicked have drawn out their swords and have bent their bows to cast down the oppressed and needy, to kill those who are upright.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Their swords will pierce their own hearts, and their bows will be broken.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Better is the little that the righteous has than the abundance of many wicked people.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
For the arms of the wicked people will be broken, but Yahweh supports the righteous people.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Yahweh watches over the blameless day by day, and their heritage will be forever.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
They will not be ashamed when times are bad. When famine comes, they will have enough to eat.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
But evil men will perish. Yahweh's enemies will be like the glory of the pastures; they will be consumed and disappear in the smoke.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
The wicked person borrows but does not repay, but the righteous person is generous and gives.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
Those who are blessed by God will inherit the land; those who are cursed by him will be cut off.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
It is by Yahweh that a man's steps are established, the man whose way is commendable in God's sight.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Though he stumbles, he will not fall down, for Yahweh is holding him with his hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
I was young and now am old; I have never seen the righteous person abandoned or his children begging for bread.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
All the day long he is gracious and lends, and his children become a blessing.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Turn away from evil and do what is right; then you will be safe forever.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
For Yahweh loves justice and does not abandon his faithful followers. They are preserved forever, but the descendants of the wicked will be cut off.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
The righteous will inherit the land and live there forever.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
The mouth of the righteous person speaks wisdom and increases justice.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
The law of his God is in his heart; his feet will not slip.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
The wicked person watches the righteous person and seeks to kill him.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Yahweh will not abandon him into the evil person's hand or condemn him when he is judged.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Wait for Yahweh and keep his way, and he will raise you up to possess the land. You will see when the wicked are cut off.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
I have seen the wicked and terrifying person spread out like a green tree in its native soil.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
But when I passed by again, he was not there. I looked for him, but he could not be found.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Observe the man of integrity, and mark the upright; there is a good future for a man of peace.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
Sinners will be totally destroyed; the future for the wicked man is cut off.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Salvation of the righteous comes from Yahweh; he protects them in the times of trouble.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Yahweh helps them and rescues them. He rescues them from evil men and saves them because they have taken refuge in him.