< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
David’s. [An Alphabetical Psalm.] Burn not with vexation because of evil-doers, Be not envious of the workers of perversity;
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
For, like grass, soon shall they wither, and, like green herbage, shall they fade.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Trust in Yahweh, and do good, Dwell in the land, and feed on fidelity;
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Yea, rest thy delight on Yahweh, that he may give thee the requests of thy heart.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Roll on Yahweh thy way, Trust also in him, and, he, will effectually work:
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
So will he bring forth, as the light, thy righteousness, and thy vindication as the noonday.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Be resigned to Yahweh, yea wait with longing for him; Burn not with vexation at him who prospereth in his way, —at the man who doeth wickedness.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Cease from anger, and forsake wrath, Burn not with vexation—[it would be] only to do evil;
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
For, evil doers, shall be cut off, but, as for them who wait for Yahweh, they, shall inherit the earth.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Yet a little, therefore, and the lawless one shall not be, Yea thou shalt look about, over his place—and he shall have vanished!
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
But, the patient oppressed-ones, shall inherit the earth, and shall delight themselves over the abundance of prosperity.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
Plotting is the lawless one, against the just, and gnashing upon him with his teeth.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
My Lord, shall laugh at him, for he seeth, that his day, will come.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
A sword, have the lawless, drawn out, and have trodden their bow, —To bring down the oppressed and the needy, To slaughter the upright in life:
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Their sword, shall enter into their own heart, and, their bow, shall be broken.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Better the little of the righteous man, than the abundance of the lawless who are mighty;
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
For, the arms of the lawless, shall be broken, But Yahweh is upholding the righteous.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Yahweh knoweth the days of the blameless, that, their inheritance, unto times age-abiding, shall continue.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
They shall not be ashamed in the time of calamity, and, in the days of famine, shall they be filled.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
For, the lawless, shall perish, and, the foes of Yahweh, be like the glory of the meadows, They have vanished! In smoke, have they vanished!
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
A lawless man borroweth, and will not repay, But, a righteous man, showeth favour and giveth;
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
For, such as are blessed of him, shall inherit the earth, But, the cursed of him, shall be cut off.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
From Yahweh, are the steps of a man made firm, When, with his way, he is well pleased:
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Though he fall, he shall not be hurled headlong, For, Yahweh, is holding his hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
Young, have I been, moreover am old, —Yet have I not seen, A righteous man forsaken, Nor his seed begging bread:
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
All day long, is he showing favour and lending, his seed, therefore, shall have a blessing.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Turn from evil, and do good, and so settle down, unto times age-abiding.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
For, Yahweh, loveth justice, and will not forsake his men of lovingkindness, Unto times age-abiding, have the perverse been destroyed, —and the seed of the lawless, been cut off.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
The righteous, shall inherit the earth, that they may settle down, to futurity, thereupon.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
The mouth of a righteous man, softly uttereth wisdom, and, his tongue, speaketh justice:
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
The law of his God, is in his heart, his steps shall not swerve.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
The lawless man, lieth in wait, for the just, and seeketh to put him to death:
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Yahweh, will not leave him in his hand, nor condemn him, when he is judged.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Wait for Yahweh, and observe thou his path, that he may exalt thee, to inherit the earth, On the cutting off of the lawless, shalt thou look.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
I have seen a lawless man, a tyrant, and spreading himself out, like a cedar in Lebanon;
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Then I passed by, and lo! he had vanished! Yea I sought him, but he could not be found.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Mark the blameless man, and behold the upright, for there is a hereafter for the man of peace;
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
But, transgressors, are to be destroyed together, the hereafter of lawless men, is to be cut off.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
But, the deliverance of the righteous, is from Yahweh, their refuge in a time of distress.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Thus hath Yahweh helped them, thus hath he delivered them, —He will deliver them from the lawless, and will save them, because they have sought refuge in him.

< Zabura 37 >