< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
“A psalm of David.” Be not thou angry on account of the wicked, Nor be envious of those who do iniquity.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
For soon shall they be cut down like grass, And wither like the green herb.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Trust in the LORD, and do good; Abide in the land, and delight in faithfulness.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Place thy delight in the LORD. And he will give thee thy heart's desires.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Commit thy way to the LORD; Trust in him, and he will give thee success!
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
He will cause thy justice to shine forth like the light, And thy righteousness like the noonday's brightness.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Hope thou patiently on the LORD, And in him place thy trust! Be not angry on account of the prosperous, —On account of him that deviseth deceit!
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Cease from anger; give not way to wrath; Be not provoked, so as to do evil!
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
For evil-doers shall be rooted out; But they who trust in the LORD, they shall inherit the land.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
Yet a little while, and the wicked shall be no more; Thou mayst look for his place, and he will not be found.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
But the meek shall inherit the land, And delight themselves in the fulness of prosperity.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
The wicked man plotteth against the just, And gnasheth at him with his teeth.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
The Lord laugheth at him; For he seeth that his day is coming.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
The wicked draw the sword, And bend their bow, To cast down the afflicted and the needy, And to slay the upright.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Their swords shall enter their own hearts, And their bows shall be broken in pieces.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Better is the little of the righteous man Than the great abundance of the wicked;
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
For the arms of the wicked shall be broken, But the LORD will uphold the righteous.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
The LORD careth for the life of the upright, And their inheritance shall endure for ever.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
They shall not be ashamed in the evil time, And in the days of famine they shall have enough.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
But the wicked shall perish; Yea, the enemies of the LORD shall be consumed, like the glory of the fields; They shall be consumed into smoke.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
The wicked borroweth, and repayeth not; But the righteous is merciful and bountiful.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
For they who are blessed by God shall inherit the land, And they who are cursed by him shall be rooted out.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
The steps of the good man are directed by the LORD; He delighteth himself in his way.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Though he fall, he shall not be utterly cast down, For the LORD holdeth him by the hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
I have been young, and now am old; Yet have I not seen the righteous forsaken, Nor his offspring begging bread.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
He is ever merciful and lendeth, And his offspring shall be blessed.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Depart from evil, and do good; So thou shalt dwell in the land for ever.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
For the LORD loveth righteousness, And forsaketh not his servants; They are preserved for ever; But the posterity of the wicked shall be rooted out.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
The righteous shall inherit the land, And shall dwell therein for ever.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
The mouth of the righteous uttereth wisdom, And his tongue speaketh what is right.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
The law of his God is in his heart; His footsteps shall not slip.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
The wicked watcheth the righteous, And seeketh to slay him;
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
The Lord will not leave him in his hand, Nor suffer him to be condemned, when he is judged.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Trust in the LORD, and keep his way, And he will exalt thee to the possession of the land, Whilst thou shalt see the destruction of the wicked!
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
I have seen a wicked man in great power, And spreading himself like a green cedar;
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
But he passed away, and, lo! he was no more; Yea, I sought him, but he was not found.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Mark the righteous man, and behold the upright, That posterity is to the man of peace!
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
But transgressors will all be destroyed; The posterity of the wicked shall be rooted out.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
The salvation of the just is from the LORD. He is their strength in the time of trouble.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
The LORD will help and deliver them; He will deliver them from their enemies, and save them, Because they trust in him.

< Zabura 37 >