< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
FRET not thyself because of evildoers, neither be thou envious against the workers of iniquity.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
For they shall soon be cut down like the grass, and wither as the green herb.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Trust in the Lord, and do good; so shalt thou dwell in the land, and verily thou shalt be fed.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Delight thyself also in the Lord; and he shall give thee the desires of thine heart.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Commit thy way unto the Lord; trust also in him; and he shall bring it to pass.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
And he shall bring forth thy righteousness as the light, and thy judgment as the noonday.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Rest in the Lord, and wait patiently for him: fret not thyself because of him who prospereth in his way, because of the man who bringeth wicked devices to pass.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Cease from anger, and forsake wrath: fret not thyself in any wise to do evil.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
For evildoers shall be cut off: but those that wait upon the Lord, they shall inherit the earth.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
For yet a little while, and the wicked shall not be: yea, thou shalt diligently consider his place, and it shall not be.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
But the meek shall inherit the earth; and shall delight themselves in the abundance of peace.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
The wicked plotteth against the just, and gnasheth upon him with his teeth.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
The Lord shall laugh at him: for he seeth that his day is coming.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
The wicked have drawn out the sword, and have bent their bow, to cast down the poor and needy, and to slay such as be of upright conversation.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Their sword shall enter into their own heart, and their bows shall be broken.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
A little that a righteous man hath is better than the riches of many wicked.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
For the arms of the wicked shall be broken: but the Lord upholdeth the righteous.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
The Lord knoweth the days of the upright: and their inheritance shall be for ever.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
They shall not be ashamed in the evil time: and in the days of famine they shall be satisfied.
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
But the wicked shall perish, and the enemies of the Lord shall be as the fat of lambs: they shall consume; into smoke shall they consume away.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
The wicked borroweth, and payeth not again: but the righteous sheweth mercy, and giveth.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
For such as be blessed of him shall inherit the earth; and they that be cursed of him shall be cut off.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
The steps of a good man are ordered by the Lord: and he delighteth in his way.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Though he fall, he shall not be utterly cast down: for the Lord upholdeth him with his hand.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
I have been young, and now am old; yet have I not seen the righteous forsaken, nor his seed begging bread.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
He is ever merciful, and lendeth; and his seed is blessed.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Depart from evil, and do good; and dwell for evermore.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
For the Lord loveth judgment, and forsaketh not his saints; they are preserved for ever: but the seed of the wicked shall be cut off.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
The righteous shall inherit the land, and dwell therein for ever.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
The mouth of the righteous speaketh wisdom, and his tongue talketh of judgment.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
The law of his God is in his heart; none of his steps shall slide.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
The wicked watcheth the righteous, and seeketh to slay him.
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
The Lord will not leave him in his hand, nor condemn him when he is judged.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Wait on the Lord, and keep his way, and he shall exalt thee to inherit the land: when the wicked are cut off, thou shalt see it.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
I have seen the wicked in great power, and spreading himself like a green bay tree.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
Yet he passed away, and, lo, he was not: yea, I sought him, but he could not be found.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Mark the perfect man, and behold the upright: for the end of that man is peace.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
But the transgressors shall be destroyed together: the end of the wicked shall be cut off.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
But the salvation of the righteous is of the Lord: he is their strength in the time of trouble.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
And the Lord shall help them, and deliver them: he shall deliver them from the wicked, and save them, because they trust in him.

< Zabura 37 >