< Zabura 37 >

1 Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
A psalm for David himself. Be not emulous of evildoers; nor envy them that work iniquity.
2 gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
For they shall shortly wither away as grass, and as the green herbs shall quickly fall.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Trust in the Lord, and do good, and dwell in the land, and thou shalt be fed with its riches.
4 Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Delight in the Lord, and he will give thee the requests of thy heart.
5 Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Commit thy way to the Lord, and trust in him, and he will do it.
6 Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
And he will bring forth thy justice as the light, and thy judgment as the noonday.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Be subject to the Lord and pray to him Envy not the man who prospereth in his way; the man who doth unjust things.
8 Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
Cease from anger, and leave rage; have no emulation to do evil.
9 Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
For the evildoers shall be cut off: but they that wait upon the Lord shall inherit the land.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
For yet a little while, and the wicked shall not be: and thou shalt seek his place, and shalt not find it.
11 Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
But the meek shall inherit the land, and shall delight in abundance of peace.
12 Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
The sinner shall watch the just man: and shall gnash upon him with his teeth.
13 amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
But the Lord shall laugh at him: for he foreseeth that his day shall come.
14 Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
The wicked have drawn out the sword: they have bent their bow. To cast down the poor and needy, to kill the upright of heart.
15 Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Let their sword enter into their own hearts, and let their bow be broken.
16 Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
Better is a little to the just, than the great riches of the wicked.
17 gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
For the arms of the wicked shall be broken in pieces; but the Lord strengtheneth the just.
18 Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
The Lord knoweth the days of undefiled; and their inheritance shall be for ever.
19 A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
They shall not be confounded in the evil time; and in the days of famine they shall be filled:
20 Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
Because the wicked shall perish. And the enemies of the Lord, presently after they shall be honoured and exalted, shall come to nothing and vanish like smoke.
21 Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
The sinner shall borrow, and not pay again; but the just sheweth mercy and shall give.
22 waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
For such as bless him shall inherit the land: but such as curse him shall perish.
23 In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
With the Lord shall the steps of a man be directed, and he shall like well his way.
24 ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
When he shall fall he shall not be bruised, for the Lord putteth his hand under him.
25 Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
I have been young, and now am old; and I have not seen the just forsaken, nor his seed seeking bread.
26 Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
He sheweth mercy, and lendeth all the day long; and his seed shall be in blessing.
27 Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
Decline from evil and do good, and dwell for ever and ever.
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
For the Lord loveth judgment, and will not forsake his saints: they shall be preserved for ever. The unjust shall be punished, and the seed of the wicked shall perish.
29 Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
But the just shall inherit the land, and shall dwell therein for evermore.
30 Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
The mouth of the just shall meditate wisdom: and his tongue shall speak judgment.
31 Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
The law of his God is in his heart, and his steps shall not be supplanted.
32 Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
The wicked watcheth the just man, and seeketh to put him to death,
33 amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
But the Lord will not leave in his hands; nor condemn him when he shall be judged.
34 Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Expect the Lord and keep his way: and he will exalt thee to inherit the land: when the sinners shall perish thou shalt see.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
I have seen the wicked highly exalted, and lifted up like the cedars of Libanus.
36 amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
And I passed by, and lo, he was not: and I sought him and his place was not found.
37 Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
Keep innocence, and behold justice: for there are remnants for the peaceable man.
38 Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
But the unjust shall be destroyed together: the remnants of the wicked shall perish.
39 Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
But the salvation of the just is from the Lord, and he is their protector in the time of trouble.
40 Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
And the Lord will help them and deliver them: and he will rescue them from the wicked, and save them, because they have hoped in him.

< Zabura 37 >