< Zabura 35 >
1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
Gospode! budi suparnik suparnicima mojim; udri one koji udaraju na me.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Uzmi oružje i štit, i digni se meni u pomoæ.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Potegni koplje, i presijeci put onima koji me gone, reci duši mojoj: ja sam spasenje tvoje.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Neka se postide i posrame koji traže dušu moju; neka se odbiju natrag i postide koji mi zlo hoæe.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Neka budu kao prah pred vjetrom, i anðeo Gospodnji neka ih progoni.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Neka bude put njihov taman i klizav, i anðeo Gospodnji neka ih tjera.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
Jer ni za što zastriješe mrežom jamu za mene, ni za što iskopaše jamu duši mojoj.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
Neka doðe na njega pogibao nenadna, i mreža koju je namjestio neka ulovi njega, neka on u nju padne na pogibao.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
A duša æe se moja radovati o Gospodu, i veseliæe se za pomoæ njegovu.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
Sve æe kosti moje reæi: Gospode! ko je kao ti, koji izbavljaš stradalca od onoga koji mu dosaðuje, i ništega i ubogoga od onoga koji ga upropašæuje?
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Ustaše na me lažni svjedoci; što ne znam, za ono me pitaju.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Plaæaju mi zlo za dobro, i sirotovanje duši mojoj.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Ja se u bolesti njihovoj oblaèih u vreæu, muèih postom dušu svoju, i molitva se moja vraæaše u prsima mojima.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
Kao prijatelj, kao brat postupah; bijah sjetan i s oborenom glavom kao onaj koji za materom žali.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
A oni se raduju kad se ja spotaknem, i kupe se, kupe se na me, zadaju rane, ne znam zašto, èupaju i ne prestaju.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
S nevaljalijem i podrugljivijem besposlièarima škrguæu na me zubima svojima.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
Gospode! hoæeš li dugo gledati? Otmi dušu moju od napadanja njihova, od ovijeh lavova jedinicu moju.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
Priznavaæu te u saboru velikom, usred mnogoga naroda hvaliæu te:
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Da mi se ne bi svetili koji mi zlobe nepravedno, i namigivali oèima koji mrze na me ni za što.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
Jer oni ne govore o miru, nego na mirne na zemlji izmišljaju lažne stvari.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
Razvaljuju na me usta svoja, i govore: dobro! dobro! vidi oko naše.
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Vidiš, Gospode! nemoj muèati; Gospode! nemoj otstupiti od mene.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Probudi se, ustani na sud moj, Bože moj i Gospode, i na parnicu moju.
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Sudi mi po pravdi svojoj, Gospode, Bože moj, da mi se ne svete.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Ne daj da govore u srcu svojem: dobro! to smo htjeli! Ne daj da govore: proždrijesmo ga.
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Nek se postide i posrame svi koji se raduju zlu mojemu, nek se obuku u stid i u sram koji se razmeæu nada mnom.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Neka se raduju i vesele koji mi žele pravdu, i govore jednako: velik Gospod, koji želi mira sluzi svojemu!
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
I moj æe jezik kazivati pravdu tvoju, i hvalu tebi svaki dan.