< Zabura 35 >

1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
Salmo de Davi: Disputa, SENHOR contra os meus adversários; luta contra os que lutam contra mim.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Pega os [teus] pequeno e grande escudos, e levanta-te em meu socorro.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
E tira a lança, e fecha [o caminho] ao encontro de meus perseguidores; dize à minha alma: Eu sou tua salvação.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Envergonhem-se, e sejam humilhados os que buscam [matar] a minha alma; tornem-se para trás, e sejam envergonhados os que planejam o mal contra mim.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Sejam como a palha perante o vento; e que o anjo do SENHOR os remova.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Que o caminho deles seja escuro e escorregadio; e o anjo do SENHOR os persiga.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
Porque sem motivo eles esconderam de mim a cova de sua rede; sem motivo eles cavaram para minha alma.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
Venha sobre ele a destruição sem que ele saiba [de antemão]; e sua rede, que ele escondeu, que o prenda; que ele, assolado, caia nela.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
E minha alma se alegrará no SENHOR; ela se encherá de alegria por sua salvação.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
Todos os meus ossos dirão: SENHOR, quem [é] como tu, que livras ao miserável daquele que é mais forte do que ele, e ao miserável e necessitado, daquele que o rouba?
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Levantam-se más testemunhas; exigem de mim [coisas] que não sei.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Ele retribuem o bem com o mal, desolando a minha alma.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Mas eu, quando ficavam doentes, minha roupa [era] de saco; eu afligia a minha alma com jejuns, e minha oração voltava ao meu seio.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
Eu agia [para com eles] como [para] um amigo [ou] irmão meu; eu andava encurvado, como que de luto pela mãe.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
Mas quando eu vacilava, eles se alegravam e se reuniam; inimigos se reuniam sem que eu soubesse; eles me despedaçavam [em palavras], e não se calavam.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Entre os fingidos zombadores [em] festas, eles rangiam seus dentes por causa de mim.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
Senhor, até quando tu [somente] observarás? Resgata minha alma das assolações deles; minha única [vida] dos filhos dos leões.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
Assim eu te louvarei na grande congregação; numa grande multidão eu celebrarei a ti.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Não se alegrem meus inimigos por causa de mim por um mau motivo, [nem] acenem com os olhos aquele que me odeiam sem motivo.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
Porque eles não falam de paz; mas sim, planejam falsidades contra os pacíficos da terra.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
E abrem suas bocas contra mim, dizendo: Ha-ha, nós vimos com nossos [próprios] olhos!
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Tu, SENHOR, tens visto [isso]; não fiques calado; SENHOR, não fiques longe de mim.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Levanta-te e acorda para meu direito, Deus meu, e Senhor meu, para minha causa.
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Julga-me conforme a tua justiça, SENHOR meu Deus; e não deixes eles se alegrarem de mim.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Não digam eles em seus corações: Ahá, [vencemos], alma nossa! nem digam: Nós já o devoramos!
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Que eles se envergonhem, e sejam juntamente humilhados os que se alegram pelo meu mal; vistam-se de vergonha e confusão os que se engrandecem contra mim.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Cantem de alegria e sejam muito contentes os que amam a minha justiça; e continuamente digam: Seja engrandecido o SENHOR, que ama o bem-estar de seu servo.
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
E minha língua falará de tua justiça, louvando a ti o dia todo.

< Zabura 35 >