< Zabura 35 >
1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
Mazmur Daud. TUHAN, lawanlah orang yang melawan aku, perangilah orang yang memerangi aku.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Ambillah utar-utar dan perisai-Mu, dan bangkitlah menolong aku.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Angkatlah lembing dan tombak-Mu untuk melawan orang yang mengejar aku. Katakanlah kepadaku bahwa Engkau penyelamatku.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Biarlah orang yang mau membunuh aku dikalahkan dan dipermalukan. Biarlah orang yang berkomplot melawan aku mundur dengan kebingungan.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Biarlah mereka diburu malaikat TUHAN, seperti sekam dihamburkan angin.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Biarlah mereka dikejar malaikat TUHAN di jalan yang gelap dan licin.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
Percuma mereka memasang perangkap bagiku atau menggali lubang untuk menangkap aku.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
Biarlah mereka ditimpa kebinasaan dengan tidak disangka-sangka. Biarlah mereka tertangkap dalam perangkapnya sendiri lalu jatuh dan binasa.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
Maka aku bersorak-sorak karena TUHAN, hatiku gembira sebab Ia menyelamatkan aku.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
Dengan segenap hati aku berkata, "TUHAN, Engkau tak ada bandingnya! Engkau melepaskan yang lemah dari yang kuat, yang miskin dan sengsara dari penindasnya."
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Saksi-saksi jahat bangkit melawan aku, dan menuduh aku melakukan hal-hal yang tidak kuketahui.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Kebaikanku mereka balas dengan kejahatan; aku tenggelam dalam keputusasaan.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Waktu mereka sakit, aku sedih dan tidak makan; aku berdoa dengan menundukkan kepala,
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
seperti mendoakan seorang saudara atau seorang sahabat karib. Aku tunduk menangisi mereka, seolah aku berkabung untuk ibuku sendiri.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
Tetapi waktu aku susah, mereka senang, dan berkerumun melawan aku. Mereka berjalan terpincang-pincang untuk menghina aku.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Mereka terus mengolok-olok seorang lumpuh, dan memandang aku dengan benci.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
Sampai kapan, ya TUHAN, sampai kapan Engkau hanya memandang saja? Selamatkanlah aku dari serangan mereka, luputkanlah nyawaku dari singa-singa itu.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
Maka aku akan bersyukur kepada-Mu di tengah umat-Mu, dan memuji nama-Mu dalam pertemuan mereka.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Jangan membiarkan aku dipermainkan oleh orang yang memusuhi aku tanpa sebab. Jangan membiarkan aku disoraki oleh orang yang membenci aku tanpa alasan.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
Bicara mereka tidak ramah; mereka merencanakan penipuan terhadap orang yang hidup rukun.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
Mereka berteriak-teriak kepadaku dan berkata bahwa mereka sudah melihat perbuatanku.
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Tetapi Engkau, TUHAN, telah melihatnya; janganlah berdiam diri, ya TUHAN, janganlah jauh daripadaku.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Bangkitlah membela perkaraku, ya Allahku dan Tuhanku, tolonglah aku!
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Belalah aku, sebab Engkau adil, ya TUHAN Allahku, jangan biarkan musuh menyoraki aku.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Jangan biarkan mereka berkata dalam hati, "Syukur, kita sudah menghabiskan nyawanya. Keinginan kita sudah terkabul!"
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Biarlah orang yang senang melihat sengsaraku menjadi bingung dan mendapat malu. Biarlah orang yang menyombongkan diri terhadapku dihina dan dipermalukan.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Semoga orang yang ingin melihat aku dibenarkan bersorak dan bergembira. Semoga mereka berulang-ulang berkata, "Sungguh agunglah TUHAN! Ia menginginkan keselamatan hamba-Nya!"
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
Maka aku akan mewartakan keadilan-Mu, dan memuji Engkau sepanjang hari.