< Zabura 35 >

1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
E HAKAKA, e Iehova, me na mea i hakaka me au: E paio oe me ka poe i paio mai ia'u,
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
E lalau i ka palekaua a me ka uhikino, A e ku mai oe iluna i kokua no'u
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Unuhi ae hoi oe i ka ihe a e keakea i ka poe alualu hewa mai ia'u: E olelo mai i kuu uhane, Owau no kou ola.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
E hoka a e hoohilahilaia ka poe i kii mai i ko'u uhane; E hoohuliia'ku lakou i hope, a e hoohokaia hoi na mea i kukakuka i ka ino no'u.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
E like lakou me ka opala imua o ka makani, A e alualu ka anela o Iehova.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
A pouli mai, a pahee hoi ko lakou alanui, A e alualu hoi ka anela a Iehova ia lakou.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
No ka mea, i ka hala ole, huua lakou i ka lakou upena no'u, Iloko o ka lua a lakou i eli ai no kuu uhane, i ka hala ole.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
E kau mai ka make ike ole ia maluna ona; A e hoohei ia ia iho kana upena i huna ai; Iloko o ua make la e haule iho ai oia.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
E hauoli ko'u uhane ia Iehova; E olioli no hoi i kona hoola ana.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
E olelo aku no hoi ka'u mau iwi a pau, E Iehova, owai la ka mea like me oe? Ka mea i hoopakele i ka mea haahaa i ka mea i oi ka ikaika i kona, Oia hoi, o ka mea ilihune me ka nele i ka mea hao wale ia ia?
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Ua ku iluna na hoike wahahee; Ua hookolokolo mai lakou ia'u ma na mea a'u i ike ole ai.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Ua uku mai lakou ia'u me ka hewa no ka pono, I haalele loa ia ko'u uhane.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Aka, owau nei la, i ko lakou mai ana, O ke kapa ino ka'u i aahu ai: A hookaumaha au i kuu uhane me ka hookeai, A ua hoi mai ka'u pule iloko o kuu poli iho.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
Ua hele au me he mea la o ko'u hoaaloha, a o ko'u hoahanau paha ia: Ua kulou iho au me ke kaumaha, E like me ka mea kanikau no kona makuwahine.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
Aka, i kuu oopa ana, olioli lakou, a akoakoa hoi, Oia hoi ua akoakoa ku e ia ia'u ka poe aki, aole hoi au i ike, Ua haehae mai lakou ia'u aole i noho malie.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Iwaena o na aia hoakaaka ma na ahaaina, Nau mai lakou i ko lakou mau niho ia'u.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
E ka Haku, pehea ka loihi o kou nana ana mai? E hoopakele i kuu uhane i ko lakou luku ana, A i ko'u makamae i na liona.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
E hoomaikai aku au ia oe iloko o ke anaina nui; E hoolea aku au ia oe iwaena o na kanaka lehulehu.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Mai noho a hauoli hewa mai ko'u mau enemi maluna o'u: A imo me ka maka ka poe inaina wale mai ia'u.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
No ka mea, aole lakou i olelo ma ke kuikahi; Ua kukakuka lakou i na mea hoopunipuni ku e i na mea noho malie ma ka aina.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
Oiaio, ua hoohamama loa lakou i ko lakou waha ia'u; I iho la lakou, Aia la! aia la! ua ike ko makou maka ia.
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Oia kau i ike mai ai, e Iehova, mai hakanu oe, E ka Haku, mai noho a mamao aku ia'u.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
E paipai ia oe iho, e ala'e hoi e hoopono ia'u; Ma kuu mea e hakaka ai, e kuu Akua, e kuu Haku hoi.
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
E hoopono mai ia'u, e Iehova kuu Akua, mamuli o kou pono; Mai noho a hauoli lakou maluna o'u.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Mai noho a olelo lakou iloko o ko lakou naau, Aia la! O ko makou makemake no ia: Mai noho a olelo lakou, Ua ale kakou ia ia.
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
E hoka a e hoohilahila pu ia no hoi ka poe hauoli i ko'u poino; E hoaahuia me ka hilahila a me ka hoinoia ka poe haanui ku e mai ia'u.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
E hooho i ka olioli a e hauoli hoi ka poe kokua i kuu pono; A e olelo mau lakou, E mahaloia'ku o Iehova, Ka mea i oluolu i ka pomaikai o kana kauwa nei.
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
A e hai aku kuu alelo i kou hoopono ana, A i ka hoolea nou a po ka la.

< Zabura 35 >