< Zabura 35 >

1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
Psaume de David. Éternel, défends-moi contre mes adversaires; combats ceux qui me combattent!
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Prends l'écu et le bouclier, et lève-toi pour me secourir!
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Saisis la lance, barre le passage à ceux qui me poursuivent; dis à mon âme: Je suis ton salut.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Qu'ils soient honteux et confus, ceux qui en veulent à ma vie; qu'ils reculent et qu'ils rougissent, ceux qui méditent mon malheur!
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Qu'ils soient comme la paille livrée au vent, et que l'ange de l'Éternel les chasse!
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Que leur chemin soit ténébreux et glissant, et que l'ange de l'Éternel les poursuive!
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
Car sans cause ils m'ont tendu leur filet sur une fosse; sans cause ils l'ont creusée pour m'ôter la vie.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
Qu'une ruine imprévue l'atteigne! Qu'il soit pris au filet qu'il a caché! Qu'il y tombe et qu'il périsse!
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
Et mon âme s'égaiera en l'Éternel, et se réjouira de sa délivrance.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
Tous mes os diront: Éternel, qui est semblable à toi, qui délivres l'affligé de celui qui est plus fort que lui, l'affligé et le pauvre de celui qui le dépouille?
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
De faux témoins se lèvent; ils me demandent des choses dont je ne sais rien.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Ils me rendent le mal pour le bien; mon âme est dans l'abandon.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Mais moi, quand ils étaient malades, je me couvrais d'un sac, j'affligeais mon âme par le jeûne, et ma prière revenait sur mon sein.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
Je marchais lentement comme pour le deuil d'un ami, d'un frère; j'allais courbé tristement comme au deuil d'une mère.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
Mais quand j'ai chancelé, ils se sont rassemblés joyeux; ils se sont rassemblés, me frappant à mon insu, me déchirant sans cesse.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Avec des impies, des bouffons de table, ils grincent les dents contre moi.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
Seigneur, jusques à quand le verras-tu? Délivre mon âme de leurs violences; arrache au lion mon unique bien!
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
Je te célébrerai dans la grande assemblée; je te louerai au milieu d'un peuple nombreux.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Que mes injustes ennemis ne se réjouissent point à mon sujet; que ceux qui me haïssent sans cause ne clignent pas l'œil!
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
Car ils ne parlent point de paix, mais ils méditent des tromperies contre les gens paisibles du pays.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
Ils ont ouvert contre moi leur bouche, disant: Ah! ah! notre œil a vu!
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Tu l'as vu, Éternel; ne te tais point!
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Seigneur, ne sois pas loin de moi! Réveille-toi, lève-toi pour me faire droit, mon Dieu, mon Seigneur, pour défendre ma cause!
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Juge-moi selon ta justice, Éternel mon Dieu, et qu'ils ne se réjouissent point de moi!
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Qu'ils ne disent pas en leur cœur: Ah! notre âme est contente! Qu'ils ne disent pas: Nous l'avons englouti!
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Qu'ils soient honteux et confus, tous ceux qui se réjouissent de mon mal! Qu'ils soient revêtus de honte et de confusion, ceux qui s'élèvent fièrement contre moi!
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Que ceux qui prennent plaisir à ma justice chantent et se réjouissent! Et que sans cesse ils disent: Magnifié soit l'Éternel, qui se plaît à la prospérité de son serviteur!
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
Alors ma langue racontera ta justice, et tous les jours elle dira tes louanges.

< Zabura 35 >