< Zabura 35 >
1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
De David. Yahweh, combats ceux qui me combattent, fais la guerre à ceux qui me font la guerre!
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Saisis le petit et le grand bouclier, et lève-toi pour me secourir!
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Tire la lance et barre le passage à mes persécuteurs; dis à mon âme: « Je suis ton salut! »
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Qu’ils soient honteux et confus ceux qui en veulent à ma vie; qu’ils reculent et rougissent ceux qui méditent ma perte!
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Qu’ils soient comme la paille au souffle du vent, et que l’ange de Yahweh les chasse devant lui!
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Que leur voie soit ténébreuse et glissante, et que l’ange de Yahweh les poursuive!
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
Car sans cause ils ont caché leur filet pour ma ruine, sans cause ils ont creusé la fosse pour me faire périr.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
Que la ruine tombe sur lui à l’improviste, que le filet qu’il a caché le saisisse, qu’il y tombe et périsse!
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
Et mon âme aura de la joie en Yahweh, de l’allégresse dans son salut.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
Tous mes os diront: « Yahweh, qui est semblable à toi, délivrant le malheureux d’un plus fort que lui, le malheureux et le pauvre de celui qui le dépouille? »
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Des témoins iniques se lèvent; ils m’accusent de choses que j’ignore.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Ils me rendent le mal pour le bien; mon âme est dans l’abandon.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Et moi, quand ils étaient malades, je revêtais un sac, j’affligeais mon âme par le jeûne, et ma prière retournait sur mon sein.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
Comme pour un ami, pour un frère, je me traînais lentement; comme pour le deuil d’une mère, je me courbais avec tristesse.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
Et maintenant que je chancelle, ils se réjouissent et s’assemblent, contre moi des calomniateurs s’assemblent à mon insu; ils me déchirent sans relâche.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Comme d’impurs parasites à la langue moqueuse, ils grincent des dents contre moi.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
Seigneur, jusques à quand le verras-tu? Arrache mon âme à leurs persécutions, ma vie à la fureur de ces lions!
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
Je te louerai dans la grande assemblée, je te célébrerai au milieu d’un peuple nombreux.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Qu’ils ne se réjouissent pas à mon sujet, ceux qui m’attaquent sans raison! Qu’ils ne clignent pas des yeux, ceux qui me haïssent sans cause!
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
Car leur langage n’est pas celui de la paix; ils méditent de perfides desseins contre les gens tranquilles du pays.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
Ils ouvrent toute large contre moi leur bouche, ils disent: « Ah! ah! notre œil a vu...! »
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Yahweh, tu le vois! Ne reste pas en silence, Seigneur, ne t’éloigne pas de moi!
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Eveille-toi, lève-toi pour me faire justice, mon Dieu et mon Seigneur, pour prendre en main ma cause!
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Juge-moi selon ta justice, Yahweh, mon Dieu, et qu’ils ne se réjouissent pas à mon sujet!
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Qu’ils ne disent pas dans leur cœur: « Notre âme est satisfaite! » qu’ils ne disent pas: « Nous l’avons englouti! »
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Qu’ils rougissent et soient confondus tous ensemble, ceux qui se réjouissent de mon malheur! Qu’ils soient couverts de honte et d’ignominie, ceux qui s’élèvent contre moi!
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Qu’ils soient dans la joie et l’allégresse, ceux qui désirent le triomphe de mon droit; et que sans cesse ils disent: « Gloire à Yahweh, qui veut la paix de son serviteur! »
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
Et ma langue célébrera ta justice, ta louange tous les jours.