< Zabura 35 >

1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
`To Dauid. Lord, deme thou hem, that anoien me; ouercome thou hem, that fiyten ayens me.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Take thou armeris and scheeld; and rise vp into help to me.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Schede out the swerd, and close togidere ayens hem that pursuen me; seie thou to my soule, Y am thin helthe.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Thei that seken my lijf; be schent, and aschamed. Thei that thenken yuels to me; be turned awei bacward, and be schent.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Be thei maad as dust bifor the face of the wynd; and the aungel of the Lord make hem streit.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Her weie be maad derknesse, and slydirnesse; and the aungel of the Lord pursue hem.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
For with out cause thei hidden to me the deth of her snare; in veyn thei dispisiden my soule.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
The snare which he knoweth not come to hym, and the takyng which he hidde take hym; and fall he in to the snare in that thing.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
But my soule schal fulli haue ioye in the Lord; and schal delite on his helthe.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
Alle my boonys schulen seie, Lord, who is lijk thee? Thou delyuerist a pore man fro the hond of his strengere; a nedi man and pore fro hem that diuersely rauischen hym.
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Wickid witnessis risynge axiden me thingis, whiche Y knewe not.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
Thei yeldiden to me yuels for goodis; bareynnesse to my soule.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
But whanne thei weren diseseful to me; Y was clothid in an heire. I mekide my soule in fastyng; and my preier schal be turned `with ynne my bosum.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
I pleside so as oure neiybore, as oure brother; Y was `maad meke so as morenynge and sorewful.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
And thei weren glad, and camen togidere ayens me; turmentis weren gaderid on me, and Y knew not.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Thei weren scaterid, and not compunct, thei temptiden me, thei scornyden me with mowyng; thei gnastiden on me with her teeth.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
Lord, whanne thou schalt biholde, restore thou my soule fro the wickidnesse of hem; `restore thou myn oon aloone fro liouns.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
I schal knowleche to thee in a greet chirche; Y schal herie thee in a sad puple.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Thei that ben aduersaries wickidli to me, haue not ioye on me; that haten me with out cause, and bikenen with iyen.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
For sotheli thei spaken pesibli to me; and thei spekynge in wrathfulnesse of erthe thouyten giles.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
And thei maden large her mouth on me; thei seiden, Wel, wel! oure iyen han sien.
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
Lord, thou hast seen, be thou not stille; Lord, departe thou not fro me.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Rise vp, and yyue tent to my doom; my God and my Lord, biholde in to my cause.
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Mi Lord God, deme thou me bi thi riytfulnesse; and haue thei not ioye on me.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Seie thei not in her hertis, Wel, wel, to oure soule; nether seie thei, We schulen deuoure hym.
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Shame thei, and drede thei togidere; that thanken for myn yuels. Be thei clothid with schame and drede; that speken yuele thingis on me.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Haue thei ful ioie, and be thei glad that wolen my riytfulnesse; and seie thei euere, The Lord be magnyfied, whiche wolen the pees of his seruaunt.
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
And my tunge schal bithenke thi riytfulnesse; al day thin heriyng.

< Zabura 35 >