< Zabura 35 >
1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
Of David - contend! O Yahweh with opponents my fight with [those who] fight with me.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Take hold of shield and body shield and arise! help my.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
And draw out a spear and lance to meet pursuers my say to self my [am] salvation your I.
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
May they be ashamed and they may be humiliated [those who] seek life my may they be turned back backwards and may they be abashed [those who] plot harm my.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
May they be like chaff before a wind and [the] angel of Yahweh pushing.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
May it be way their darkness and slippery places and [the] angel of Yahweh pursuing them.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
For without cause they have hidden for me [the] pit of net their without cause they have dug for life my.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
May it come to him destruction [which] not he knows and net his which he hid may it catch him in destruction may he fall in it.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
And self my it will rejoice in Yahweh it will exult in salvation his.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
All bones my - they will say O Yahweh who? [is] like you [one who] delivers a poor [person] from a person [too] strong for him and [the] poor and [the] needy from [one who] robs him.
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
They rise up! witnesses of violence [that] which not I know they ask me.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
They repay me harm in place of good bereavement [belongs] to self my.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
And I - when were sick they clothing my [was] sackcloth I humbled with fasting self my and prayer my to bosom my it returned.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
Like a friend like a brother of me I went about like a mourner of a mother mourning I bowed.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
And at stumbling my they rejoiced and they gathered they gathered on me smitten [people] and not I knew they tore and not they were still.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Godless [ones] of mockers of cake they gnashed towards me teeth their.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
O Lord how long? will you look bring back! life my from ravages their from young lions only [life] my.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
I will give thanks to you in [the] assembly great among a people numerous I will praise you.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
May not they rejoice to me enemies my falsehood [those who] hate me without cause let them wink an eye.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
For not peace they speak and on [the] quiet [people] of [the] land words of deceit they plan!
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
And they have opened wide on me mouth their they have said aha! - aha! it has seen eyes our.
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
You have seen O Yahweh may not you be silent O Lord may not you be distant from me.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Wake up! and awake! for judgment my O God my and O Lord for cause my.
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Vindicate me according to righteousness your O Yahweh God my and may not they rejoice to me.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
May not they say in heart their aha! desire our may not they say we have swallowed him.
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
May they be ashamed and they may be abashed - altogether [the] [people] joyful of distress my may they be clothed shame and ignominy who magnify themselves on me.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
May they shout for joy and they may rejoice [the] [people] desirous of righteousness my and may they say continually may he be great Yahweh desiring [the] welfare of servant his.
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
And tongue my it will utter righteousness your all the day praise your.