< Zabura 35 >

1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
[By David.] Contend, YHWH, with those who contend with me. Fight against those who fight against me.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Take hold of shield and buckler, and stand up for my help.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Brandish the spear and block those who pursue me. Tell my soul, "I am your salvation."
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
Let those who seek after my soul be disappointed and brought to dishonor. Let those who plot my ruin be turned back and confounded.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
Let them be as chaff before the wind, YHWH's angel driving them on.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
Let their way be dark and slippery, YHWH's angel pursuing them.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
For without cause they have hidden their net in a pit for me. Without cause they have dug a pit for my soul.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
Let destruction come on him unawares. Let his net that he has hidden catch himself. Let him fall into that destruction.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
My soul shall be joyful in YHWH. It shall rejoice in his salvation.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
All my bones shall say, "YHWH, who is like you, who delivers the poor from him who is too strong for him; yes, the poor and the needy from him who robs him?"
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Unrighteous witnesses rise up. They ask me about things that I do not know about.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
They reward me evil for good, to the bereaving of my soul.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
But as for me, when they were sick, my clothing was sackcloth. I afflicted my soul with fasting; and my prayer returned into my own bosom.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
I behaved myself as though it had been my friend or my brother. I bowed down mourning, as one who mourns his mother.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
But in my adversity, they rejoiced, and gathered themselves together. The attackers gathered themselves together against me, and I did not know it. They tore at me, and did not cease.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
When I tripped, they mocked me relentlessly; they gnashed their teeth at me.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
YHWH, how long will you look on? Rescue my soul from their destruction, my precious life from the lions.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
I will give you thanks in the great assembly. I will praise you among many people.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Do not let those who are my enemies wrongfully rejoice over me; neither let those who hate me without a cause and wink their eyes.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
For they do not speak peace, but they devise deceitful words against those who are quiet in the land.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
Yes, they opened their mouth wide against me. They said, "Aha. Aha. Our eye has seen it."
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
You have seen it, YHWH. Do not keep silent. YHWH, do not be far from me.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Wake up. Rise up to defend me, my God. My Lord, contend for me.
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Vindicate me, YHWH my God, according to your righteousness. Do not let them gloat over me.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Do not let them say in their heart, "Aha. Aha. Our desire." Do not let them say, "We have swallowed him up."
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
Let them be put to shame and confounded together who rejoice at my calamity. Let them be clothed with shame and dishonor who magnify themselves against me.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
Let them shout for joy and be glad, who favor my righteous cause. And let them say continually, "YHWH be magnified, who delights in the peace of his servant."
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
My tongue shall talk about your righteousness and about your praise all day long.

< Zabura 35 >