< Zabura 35 >
1 Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
Of David. Contend with my opponents, O LORD; fight against those who fight against me.
2 Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
Take up Your shield and buckler; arise and come to my aid.
3 Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
Draw the spear and javelin against my pursuers; say to my soul: “I am your salvation.”
4 Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
May those who seek my life be disgraced and put to shame; may those who plan to harm me be driven back and confounded.
5 Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
May they be like chaff in the wind, as the angel of the LORD drives them away.
6 bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
May their path be dark and slick, as the angel of the LORD pursues.
7 Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
For without cause they laid their net for me; without reason they dug a pit for my soul.
8 bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
May ruin befall them by surprise; may the net they hid ensnare them; may they fall into the hazard they created.
9 Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
Then my soul will rejoice in the LORD and exult in His salvation.
10 Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
All my bones will exclaim, “Who is like You, O LORD, who delivers the afflicted from the aggressor, the poor and needy from the robber?”
11 Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
Hostile witnesses come forward; they make charges I know nothing about.
12 Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
They repay me evil for good, to the bereavement of my soul.
13 Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
Yet when they were ill, I put on sackcloth; I humbled myself with fasting, but my prayers returned unanswered.
14 nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
I paced about as for my friend or brother; I was bowed down with grief, like one mourning for his mother.
15 Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
But when I stumbled, they assembled in glee; they gathered together against me. Assailants I did not know slandered me without ceasing.
16 Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
Like godless jesters at a feast, they gnashed their teeth at me.
17 Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
How long, O Lord, will You look on? Rescue my soul from their ravages, my precious life from these lions.
18 Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
Then I will give You thanks in the great assembly; I will praise You among many people.
19 Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Let not my enemies gloat over me without cause, nor those who hate me without reason wink in malice.
20 Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
For they do not speak peace, but they devise deceitful schemes against those who live quietly in the land.
21 Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
They gape at me and say, “Aha, aha! Our eyes have seen!”
22 Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
O LORD, You have seen it; be not silent. O Lord, be not far from me.
23 Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
Awake and rise to my defense, to my cause, my God and my Lord!
24 Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
Vindicate me by Your righteousness, O LORD my God, and do not let them gloat over me.
25 Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
Let them not say in their hearts, “Aha, just what we wanted!” Let them not say, “We have swallowed him up!”
26 Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
May those who gloat in my distress be ashamed and confounded; may those who exalt themselves over me be clothed in shame and reproach.
27 Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
May those who favor my vindication shout for joy and gladness; may they always say, “Exalted be the LORD who delights in His servant’s well-being.”
28 Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.
Then my tongue will proclaim Your righteousness and Your praises all day long.