< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Zaburi ya Daudi, alipojifanya mwendawazimu mbele ya Abimeleki, ambaye alimfukuza, naye akaondoka. Nitamtukuza Bwana nyakati zote, sifa zake zitakuwa midomoni mwangu siku zote.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Nafsi yangu itajisifu katika Bwana, walioonewa watasikia na wafurahi.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Mtukuzeni Bwana pamoja nami, naam, na tulitukuze jina lake pamoja.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Nilimtafuta Bwana naye akanijibu, akaniokoa kwenye hofu zangu zote.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Wale wamtazamao hutiwa nuru, nyuso zao hazifunikwi na aibu kamwe.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Maskini huyu alimwita Bwana, naye akamsikia, akamwokoa katika taabu zake zote.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Malaika wa Bwana hufanya kituo akiwazunguka wale wamchao, naye huwaokoa.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Onjeni mwone kwamba Bwana ni mwema, heri mtu yule anayemkimbilia.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Mcheni Bwana enyi watakatifu wake, kwa maana wale wamchao hawapungukiwi na chochote.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Wana simba wenye nguvu hutindikiwa na kuona njaa, bali wale wamtafutao Bwana hawatakosa kitu chochote kilicho chema.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Njooni, watoto wangu, mnisikilize, nitawafundisha kumcha Bwana.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Yeyote kati yenu anayependa uzima na kutamani kuziona siku nyingi njema,
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
basi auzuie ulimi wake na mabaya, na midomo yake kutokana na kusema uongo.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Aache uovu, atende mema, aitafute amani na kuifuatilia.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Macho ya Bwana huwaelekea wenye haki, na masikio yake yako makini kusikiliza kilio chao.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
Uso wa Bwana uko kinyume na watendao maovu, ili kufuta kumbukumbu lao duniani.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Wenye haki hulia, naye Bwana huwasikia, huwaokoa katika taabu zao zote.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Bwana yu karibu na waliovunjika moyo, na huwaokoa waliopondeka roho.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Mwenye haki ana mateso mengi, lakini Bwana humwokoa nayo yote,
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
huhifadhi mifupa yake yote, hata mmoja hautavunjika.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Ubaya utamuua mtu mwovu, nao adui za mwenye haki watahukumiwa.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Bwana huwakomboa watumishi wake, yeyote anayemkimbilia yeye hatahukumiwa kamwe.

< Zabura 34 >