< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Bendeciré al Señor en todo momento; su alabanza estará siempre en mi boca.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Mi alma dirá grandes cosas del Señor: los mansos lo oirán, lo conocerán y se alegrarán.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
¡Alaban al Señor conmigo! Exaltemos juntos su gran nombre.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Estaba buscando al Señor, y él escuchó mi voz y me liberó de todos mis temores.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Los que vuelven sus ojos hacia él y quedan radiantes de alegría, y sus rostros no serán avergonzado.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Este pobre gritó delante del Señor, le oyó, y le dio la salvación de todos sus problemas.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
El ángel del Señor velará siempre a los que le temen, para que estén a salvo.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Prueben, verán que el Señor es bueno; Feliz es el hombre que confía en él.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Honren a Jehová, todos ustedes sus santos; para aquellos que lo hagan no tendrán necesidad de nada.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Los leoncillos están necesitados y no tienen comida; pero aquellos que buscan al Señor tendrán todo lo bueno.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Vengan, niños, presten atención a mí; Seré tu maestro en el temor del Señor.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
¿Qué hombre tiene amor por la vida, y un deseo de que sus días se incrementen para que pueda ver el bien?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Guarda tu lengua del mal, y tus labios de palabras de engaño.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Apártate del mal, y haz el bien; busca la paz, deseándola con todo tu corazón.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Los ojos del Señor están sobre los justos. y sus oídos están atentos a su clamor.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
El rostro del Señor contra los que hacen el mal, para borrar de la tierra la memoria de ellos.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
El clamor de los justos viene delante del Señor, y él los oye, los saca de todas sus angustias.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
El Señor está cerca de los quebrantados de corazón; él es el salvador de aquellos cuyos espíritus son contritos.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Grandes son los males de los justos; pero el Señor lo saca a salvo de todos ellos.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Él guarda todos sus huesos; ni uno solo le romperán.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
El mal pondrá fin al pecador, y los que aborrecen la justicia vendrán a la destrucción.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
El Señor será el salvador de las almas de sus siervos, y nadie que confía en él será avergonzado.