< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Por David; cuando fingió estar loco ante Abimelec, quien lo expulsó, y él se marchó. Bendeciré a Yahvé en todo momento. Su alabanza siempre estará en mi boca.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Mi alma se jactará en Yahvé. Los humildes lo oirán y se alegrarán.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Oh, engrandece a Yahvé conmigo. Exaltemos juntos su nombre.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Busqué a Yahvé y me respondió, y me libró de todos mis temores.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Lo miraron y quedaron radiantes. Sus rostros nunca se cubrirán de vergüenza.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Este pobre hombre clamó, y Yahvé lo escuchó, y lo salvó de todos sus problemas.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
El ángel de Yahvé acampa alrededor de los que le temen, y los entrega.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Oh, probad y ved que Yahvé es bueno. Dichoso el hombre que se refugia en él.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Temed a Yahvé, vosotros sus santos, porque no hay falta con los que le temen.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Los leones jóvenes carecen y sufren hambre, pero a los que buscan a Yahvé no les faltará nada bueno.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Venid, niños, escuchadme. Te enseñaré el temor de Yahvé.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Que es alguien que desea la vida, y ama muchos días, para que vea el bien?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Guarda tu lengua del mal, y tus labios de decir mentiras.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Apártate del mal y haz el bien. Busca la paz y persíguela.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Los ojos de Yahvé están hacia los justos. Sus oídos escuchan su grito.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
El rostro de Yahvé está contra los que hacen el mal, para cortar su memoria de la tierra.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Los justos claman, y Yahvé los escucha, y los libra de todos sus problemas.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Yahvé está cerca de los que tienen el corazón roto, y salva a los que tienen el espíritu abatido.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Muchas son las aflicciones de los justos, pero Yahvé lo libra de todos ellos.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Protege todos sus huesos. Ninguno de ellos está roto.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
El mal matará a los malvados. Los que odian a los justos serán condenados.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Yahvé redimeel alma de sus siervos. Ninguno de los que se refugian en él será condenado.