< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Blagosiljam Gospoda u svako doba, hvala je njegova svagda u ustima mojima.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Gospodom se hvali duša moja; neka èuju koji stradaju, pa neka se raduju.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Velièajte Gospoda sa mnom, uzvišujmo ime njegovo zajedno.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Tražih Gospoda, i èu me, i svijeh nevolja mojih oprosti me.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Koji u njega gledaju prosvjetljuju se, i lica se njihova neæe postidjeti.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Ovaj stradalac zavika, i Gospod ga èu, i oprosti ga svijeh nevolja njegovijeh.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Anðeli Gospodnji stanom stoje oko onijeh koji se njega boje, i izbavljaju ih.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Ispitajte i vidite kako je dobar Gospod; blago èovjeku koji se uzda u nj.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Bojte se Gospoda, sveti njegovi; jer koji se njega boje, njima nema oskudice.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Lavovi su ubogi i gladni, a koji traže Gospoda, ne premièe im se nijednoga dobra.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Hodite, djeco, poslušajte me; nauèiæu vas strahu Gospodnjemu.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Koji èovjek želi života, ljubi dane da bi vidio dobro?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Ustavljaj jezik svoj oda zla, i usta svoja od prijevarne rijeèi.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Kloni se oda zla, i èini dobro, traži mira i idi za njim.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Oèi su Gospodnje obraæene na pravednike, i uši njegove na jauk njihov.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
Ali je strašno lice Gospodnje za one koji èine zlo, da bi istrijebio na zemlji spomen njihov.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Vièu pravedni, i Gospod ih èuje, i izbavlja ih od svijeh nevolja njihovijeh.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Gospod je blizu onijeh koji su skrušena srca, i pomaže onima koji su smjerna duha.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Mnogo nevolje ima pravednik, ali ga od svijeh izbavlja Gospod.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Èuva Gospod sve kosti njegove, nijedna se od njih neæe slomiti.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Bezbožnika ubiæe zlo, i koji nenavide pravednika prevariæe se.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Gospod iskupljuje dušu sluga svojih, i koji se god u njega uzdaju, neæe se prevariti.

< Zabura 34 >