< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Davidi, cum immutavit vultum suum coram Achimelech, et dimisit eum et abiit. Benedicam Dominum in omni tempore: semper laus eius in ore meo.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
In Domino laudabitur anima mea: audiant mansueti, et lætentur.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Magnificate Dominum mecum: et exaltemus nomen eius in idipsum.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Exquisivi Dominum, et exaudivit me: et ex omnibus tribulationibus meis eripuit me.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Accedite ad eum, et illuminamini: et facies vestræ non confundentur.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Iste pauper clamavit, et Dominus exaudivit eum: et de omnibus tribulationibus eius salvavit eum.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Immittet angelus Domini in circuitu timentium eum: et eripiet eos.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Gustate, et videte quoniam suavis est Dominus: beatus vir, qui sperat in eo.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Timete Dominum omnes sancti eius: quoniam non est inopia timentibus eum.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Divites eguerunt et esurierunt: inquirentes autem Dominum non minuentur omni bono.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Venite filii, audite me: timorem Domini docebo vos.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Quis est homo qui vult vitam: diligit dies videre bonos?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Prohibe linguam tuam a malo: et labia tua ne loquantur dolum.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Diverte a malo, et fac bonum: inquire pacem, et persequere eam.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Oculi Domini super iustos: et aures eius in preces eorum.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
Vultus autem Domini super facientes mala: ut perdat de terra memoriam eorum.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Clamaverunt iusti, et Dominus exaudivit eos: et ex omnibus tribulationibus eorum liberavit eos.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Iuxta est Dominus iis, qui tribulato sunt corde: et humiles spiritu salvabit.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Multæ tribulationes iustorum: et de omnibus his liberabit eos Dominus.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Custodit Dominus omnia ossa eorum: unum ex his non conteretur.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Mors peccatorum pessima: et qui oderunt iustum delinquent.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Redimet Dominus animas servorum suorum: et non delinquent omnes qui sperant in eo.