< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Von David, als er seinen Verstand vor Abimelech verstellte, und der ihn forttrieb, und er von dannen ging. Ich will Jahwe preisen alle Zeit, sein Lob soll beständig in meinem Munde sein.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Jahwes soll sich meine Seele rühmen; die Elenden sollen es hören und sich freuen.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Verherrlicht Jahwe mit mir und laßt uns miteinander seinen Namen erheben!
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
So oft ich Jahwe suchte, erhörte er mich und aus allem, was ich gefürchtet, errettete er mich.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Die auf ihn blickten, wurden leuchtenden Angesichts, und ihr Antlitz brauchte nicht zu erblassen.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Hier ist so ein Elender, welcher rief, und Jahwe hörte und half ihm aus allen seinen Nöten.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Der Engel Jahwes lagert sich rings um die, die ihn fürchten, und reißt sie heraus.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Schmeckt und seht, daß Jahwe gütig ist; wohl dem Manne, der bei ihm Zuflucht sucht!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Fürchtet Jahwe, ihr, seine Heiligen; denn die ihn fürchten, haben keinen Mangel.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Junge Löwen darben und hungern; aber die, die Jahwe suchen, haben keinen Mangel an irgend einem Gut.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Kommt, Kinder, hört mir zu; ich will euch die Furcht Jahwes lehren!
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Wer ist der Mann, der Leben begehrt, zahlreiche Lebenstage wünscht, um Glück zu erleben?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Wahre deine Zunge vor Bösem und deine Lippen vor trügerischer Rede!
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Halte dich fern vom Bösen und thue Gutes, suche Frieden und jage ihm nach!
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Das Antlitz Jahwes ist wider die, die Böses thun, daß er ihr Gedächtnis von der Erde vertilge.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
Die Augen Jahwes sind auf die Frommen gerichtet, und seine Ohren auf ihr Geschrei.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Sie schrieen und Jahwe hörte und rettete sie aus allen ihren Nöten.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Jahwe ist denen nahe, die zerbrochenes Herzens sind, und hilft denen, die ein zerschlagenes Gemüt haben.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Zahlreich sind die Leiden des Frommen, aber Jahwe errettet ihn aus allen.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Er behütet alle seine Gebeine, daß ihrer keines zerbrochen wird.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Den Gottlosen wird das Unheil töten, und die den Frommen hassen, werden büßen.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Jahwe erlöst die Seele seiner Knechte, und alle, die bei ihm Zuflucht suchen, werden nicht büßen.