< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Psaume de David, sur ce qu'il changea son extérieur en la présence d'Abimélec, qui le chassa, et il s'en alla. [Aleph.] Je bénirai l'Eternel en tout temps, sa louange sera continuellement en ma bouche.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
[Beth.] Mon âme se glorifiera en l'Eternel; les débonnaires l'entendront, et s'en réjouiront.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
[Guimel.] Magnifiez l'Eternel avec moi, et exaltons son Nom tous ensemble.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
[Daleth.] J'ai cherché l'Eternel, et il m'a répondu, et m'a délivré de toutes mes frayeurs.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
[He. Vau.] L'a-t-on regardé? on en est illuminé, et leurs faces ne sont point confuses.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
[Zain.] Cet affligé a crié, et l'Eternel l'a exaucé, et l'a délivré de toutes ses détresses.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
[Heth.] L'Ange de l'Eternel se campe tout autour de ceux qui le craignent, et les garantit.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
[Teth.] Savourez, et voyez que l'Eternel est bon; ô que bienheureux est l'homme qui se confie en lui!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
[Jod.] Craignez l'Eternel vous ses Saints; car rien ne manque à ceux qui le craignent.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
[Caph.] Les lionceaux ont disette, ils ont faim; mais ceux qui cherchent l'Eternel n'auront besoin d'aucun bien.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
[Lamed.] Venez, enfants, écoutez-moi; je vous enseignerai la crainte de l'Eternel.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
[Mem.] Qui est l'homme qui prenne plaisir à vivre, [et] qui aime la longue vie pour voir du bien?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
[Nun.] Garde ta langue de mal, et tes lèvres de parler avec tromperie.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
[Samech.] Détourne-toi du mal, et fais le bien; cherche la paix et la poursuis.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
[Hajin.] Les yeux de l'Eternel sont sur les justes, et ses oreilles sont attentives à leur cri.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
[Pe.] La face de l'Eternel est contre ceux qui font le mal, pour exterminer de la terre leur mémoire.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
[Tsade.] Quand les justes crient, l'Eternel les exauce, et il les délivre de toutes leurs détresses.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
[Koph.] L'Eternel [est] près de ceux qui ont le cœur déchiré [par la douleur], et il délivre ceux qui ont l'esprit abattu.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
[Res.] Le juste a des maux en grand nombre, mais l'Eternel le délivre de tous.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
[Scin.] Il garde tous ses os, [et] pas un n'en est cassé.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
[Thau.] La malice fera mourir le méchant; et ceux qui haïssent le juste seront détruits.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
[Pe.] L'Eternel rachète l'âme de ses serviteurs; et aucun de ceux qui se confient en lui, ne sera détruit.

< Zabura 34 >