< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
De David, quand il dissimula sa raison devant Abimélec, qui le chassa, et il s’en alla. Je bénirai l’Éternel en tout temps; sa louange sera continuellement dans ma bouche.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Mon âme se glorifiera en l’Éternel; les débonnaires l’entendront, et se réjouiront.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Magnifiez l’Éternel avec moi, et exaltons ensemble son nom.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
J’ai cherché l’Éternel; et il m’a répondu, et m’a délivré de toutes mes frayeurs.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Ils ont regardé vers lui, et ils ont été illuminés, et leurs faces n’ont pas été confuses.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Cet affligé a crié; et l’Éternel l’a entendu, et l’a sauvé de toutes ses détresses.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
L’ange de l’Éternel campe autour de ceux qui le craignent, et les délivre.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Goûtez et voyez que l’Éternel est bon! Bienheureux l’homme qui se confie en lui!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Craignez l’Éternel, vous ses saints; car rien ne manque à ceux qui le craignent.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Les lionceaux souffrent disette, et ont faim; mais ceux qui cherchent l’Éternel ne manquent d’aucun bien.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Venez, fils, écoutez-moi: je vous enseignerai la crainte de l’Éternel.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Qui est l’homme qui prenne plaisir à la vie [et] qui aime les jours pour voir du bien?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Garde ta langue du mal, et tes lèvres de proférer la tromperie;
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Retire-toi du mal, et fais le bien; cherche la paix, et poursuis-la.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Les yeux de l’Éternel [regardent] vers les justes, et ses oreilles sont [ouvertes] à leur cri.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
La face de l’Éternel est contre ceux qui font le mal, pour retrancher de la terre leur mémoire.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
[Les justes] crient, et l’Éternel entend, et il les délivre de toutes leurs détresses.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
L’Éternel est près de ceux qui ont le cœur brisé, et il sauve ceux qui ont l’esprit abattu.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Les maux du juste sont en grand nombre; mais l’Éternel le délivre de tous:
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Il garde tous ses os, pas un d’eux n’est cassé.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Le mal fera mourir le méchant; et ceux qui haïssent le juste en porteront la peine.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
L’Éternel rachète l’âme de ses serviteurs; et aucun de ceux qui se confient en lui ne sera tenu pour coupable.

< Zabura 34 >