< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
I will always thank Yahweh; I will constantly praise him [MTY].
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
I will boast about what Yahweh [has done]. All those who are oppressed/discouraged should hear me and rejoice.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Join with me in telling others that Yahweh is great! You and I should together proclaim how glorious he is!
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
I prayed to Yahweh, and he (answered my prayer/did what I asked him to do); he rescued me from [all those who caused me] to be afraid.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Those who trust [IDM] that he [will help them] will be joyful; (they will never be disappointed/he will always do for them the things that he promises) [LIT].
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
I was miserable/helpless, but I called out to Yahweh, and he heard me. He rescued me from all my troubles.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
An angel from Yahweh guards those who revere him, and the angel rescues them.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Find out for yourself, and you will experience that Yahweh is good to you! He is very pleased with those who ask him to protect them.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
All you who belong to him, revere him! Those who do that will always have the things that they need [LIT].
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Lions [are usually] very strong, [but sometimes] even young lions are hungry and become weak, but those who trust in Yahweh will (have everything/not lack any good thing) [LIT] [that they need].
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
You (who are my students/whom I teach), come and listen to me, and I will teach you how to revere Yahweh.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
If [RHQ] any of you wants to enjoy life and have a good long life,
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
do not say anything that is evil! Do not tell lies!
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Turn away from doing evil, and do what is good! Always try hard to enable people to live peacefully [with each other.]
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Yahweh [MTY] carefully watches over those who [act] righteously; he always responds [MTY] to them when they call [to him for help].
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
But Yahweh [SYN] (is opposed to/turns away from) those who do what is evil. [And after they die], people will forget them completely.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Yahweh hears righteous people when they call out to him; he rescues them from all their troubles.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Yahweh is always ready to help those who are discouraged; he rescues those who have nothing good to hope for.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Righteous people may have many troubles, but Yahweh rescues them from all those troubles.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Yahweh protects them from being harmed; [when their enemies attack them], they will not break any bones of those righteous people.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Wicked people will be killed by their own evil deeds (OR, by [people doing to them] the same evil things [that the wicked do to others]) [PRS], and Yahweh will punish those who oppose righteous people.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Yahweh will save those who serve him. He will (not condemn/forgive) [LIT] those who trust in him.

< Zabura 34 >