< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
“A psalm of David, when he feigned himself mad before Abimelech, who drove him away, and he departed.” I will bless the LORD at all times; His praise shall continually be in my mouth.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
In the LORD doth my soul boast; Let the afflicted hear, and rejoice!
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
O magnify the LORD with me, And let us exalt his name together!
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
I sought the LORD, and he heard me, And delivered me from all my fears.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Look up to him, and ye shall have light; Your faces shall never be ashamed.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
This afflicted man cried, and the LORD heard, And saved him from all his troubles.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
The angels of the LORD encamp around those who fear him, And deliver them.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
O taste, and see how good is the LORD! Happy the man who trusteth in him!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
O fear the LORD, ye his servants! For to those who fear him there shall be no want.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Young lions want, and suffer hunger; But they who fear the LORD want no good thing.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Come, ye children, hearken to me! I will teach you the fear of the LORD.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Who is he that loveth life, And desireth many days, in which he may see good?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Guard well thy tongue from evil, And thy lips from speaking guile!
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Depart from evil, and do good; Seek peace, and pursue it!
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
The eyes of the LORD are upon the righteous, And his ears are open to their cry.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
But the face of the LORD is against evil-doers, To cut off their remembrance from the earth.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
The righteous cry, and the LORD heareth, And delivereth them from all their troubles.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
The LORD is near to them that are of a broken heart, And saveth such as are of a contrite spirit.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Many are the afflictions of the righteous; But the LORD delivereth him from them all.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
He guardeth all his bones; Not one of them shall be broken.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Calamity destroyeth the wicked, And they who hate the righteous suffer for it.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
The LORD redeemeth the life of his servants, And none that put their trust in him will suffer for it.

< Zabura 34 >