< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
BY DAVID, IN HIS CHANGING HIS BEHAVIOR BEFORE ABIMELECH, AND HE DRIVES HIM AWAY, AND HE GOES. [ALEPH-BET] I bless YHWH at all times, His praise [is] continually in my mouth.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
In YHWH my soul boasts herself, The humble hear and rejoice.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Ascribe greatness to YHWH with me, And we exalt His Name together.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
I sought YHWH, and He answered me, And delivered me from all my fears.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
They looked expectingly to Him, And they became bright, And their faces are not ashamed.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
This poor [one] called, and YHWH heard, And saved him from all his distresses.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
A messenger of YHWH is encamping, Around those who fear Him, And He arms them.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Taste and see that YHWH [is] good, O the blessedness of the man who trusts in Him.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Fear YHWH, you His holy ones, For there is no lack to those fearing Him.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Young lions have lacked and been hungry, And those seeking YHWH do not lack any good,
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Come, children, listen to me, I teach you the fear of YHWH.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Who [is] the man that is desiring life? Loving days to see good?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Keep your tongue from evil, And your lips from speaking deceit.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Turn aside from evil and do good, Seek peace and pursue it.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
The eyes of YHWH [are] to the righteous, And His ears to their cry.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
(The face of YHWH [is] on doers of evil, To cut off their memorial from earth.)
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
They cried, and YHWH heard, And delivered them from all their distresses.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
YHWH [is] near to the broken of heart, And He saves the bruised of spirit.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Many [are] the afflictions of the righteous, YHWH delivers him out of them all.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
He is keeping all his bones, Not one of them has been broken.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Evil puts the wicked to death, And those hating the righteous are desolate.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
YHWH redeems the soul of His servants, And none trusting in Him are desolate!