< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
A Psalm of David; when he changed his demeanour before Abimelech, who drove him away, and he departed. I will bless the LORD at all times; His praise shall continually be in my mouth.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
My soul shall glory in the LORD; the humble shall hear thereof, and be glad.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
O magnify the LORD with me, and let us exalt His name together.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
I sought the LORD, and He answered me, and delivered me from all my fears.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
They looked unto Him, and were radiant; and their faces shall never be abashed.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
This poor man cried, and the LORD heard, and saved him out of all his troubles.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
The angel of the LORD encampeth round about them that fear Him, and delivereth them.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
O consider and see that the LORD is good; happy is the man that taketh refuge in Him.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
O fear the LORD, ye His holy ones; for there is no want to them that fear Him.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
The young lions do lack, and suffer hunger; but they that seek the LORD want not any good thing.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Come, ye children, hearken unto me; I will teach you the fear of the LORD.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Who is the man that desireth life, and loveth days, that he may see good therein?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Keep thy tongue from evil, and thy lips from speaking guile.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Depart from evil, and do good; seek peace, and pursue it.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
The eyes of the LORD are toward the righteous, and His ears are open unto their cry.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
The face of the LORD is against them that do evil, to cut off the remembrance of them from the earth.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
They cried, and the LORD heard, and delivered them out of all their troubles.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
The LORD is nigh unto them that are of a broken heart, and saveth such as are of a contrite spirit.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Many are the ills of the righteous, but the LORD delivereth him out of them all.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
He keepeth all his bones; not one of them is broken.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Evil shall kill the wicked; and they that hate the righteous shall be held guilty.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
The LORD redeemeth the soul of His servants; and none of them that take refuge in Him shall be desolate.

< Zabura 34 >