< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
[A Psalm] of David; when he changed his behaviour before Abimelech, who drove him away, and he departed. I will bless Jehovah at all times; his praise shall continually be in my mouth.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
My soul shall make its boast in Jehovah: the meek shall hear, and rejoice.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Magnify Jehovah with me, and let us exalt his name together.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
I sought Jehovah, and he answered me, and delivered me from all my fears.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
They looked unto him, and were enlightened, and their faces were not confounded.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
This afflicted one called, and Jehovah heard [him], and saved him out of all his troubles.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
The angel of Jehovah encampeth round about them that fear him, and delivereth them.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Taste and see that Jehovah is good: blessed is the man that trusteth in him!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Fear Jehovah, ye his saints; for there is no want to them that fear him.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
The young lions are in need and suffer hunger; but they that seek Jehovah shall not want any good.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Come, ye sons, hearken unto me: I will teach you the fear of Jehovah.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
What man is he that desireth life, [and] loveth days, that he may see good?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Keep thy tongue from evil, and thy lips from speaking guile;
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Depart from evil, and do good; seek peace, and pursue it.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
The eyes of Jehovah are upon the righteous, and his ears are toward their cry;
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
The face of Jehovah is against them that do evil, to cut off the remembrance of them from the earth:
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
[The righteous] cry, and Jehovah heareth, and delivereth them out of all their troubles.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Jehovah is nigh to those that are of a broken heart, and saveth them that are of a contrite spirit.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Many are the adversities of the righteous, but Jehovah delivereth him out of them all:
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
He keepeth all his bones; not one of them is broken.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Evil shall destroy the wicked; and they that hate the righteous shall bear their guilt.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Jehovah redeemeth the soul of his servants; and none of them that trust in him shall bear guilt.