< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Співайте із радістю, праведні в Господі, — бо щи́рим лицю́є хвала́!
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Хваліть Господа гу́слами, співайте Йому з десятистру́нною а́рфою,
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
заспівайте Йому нову пісню, гарно заграйте Йому з гуком су́рем,
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
бо щире Господнєє слово, і кожен чин Його вірний!
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Правду та суд Він коха́є, і Господньої милости повна земля!
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Словом Господнім учи́нене небо, а подихом уст Його все його ві́йсько.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Воду мо́рську збирає Він, мов би до мі́ху, безо́дні складає в комо́рах.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Буде боятися Господа ці́ла земля, всі ме́шканці все́світу бу́дуть лякатись Його,
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
бо сказав Він — і сталось, наказав — і з'явилось.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Госпо́дь ра́ду пога́нів пони́щить, поні́вечить ми́слі наро́дів,
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
а за́дум Господній навіки стоятиме, думки́ Його серця — на вічні віки́!
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Блаженний той люд, що Богом у нього Госпо́дь, блаженний наро́д, що Він вибрав його на спа́док Собі!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Господь споглядає з небе́с, і бачить усіх синів лю́дських,
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
приглядається з місця оселі Своєї до всіх, хто замешкує землю:
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Хто створив серце кожного з них, наглядає всі їхні діла́!
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Немає царя, що його многість ві́йська спасає, не врятується ве́летень вели́кістю сили,
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
для спасі́ння той кінь ненадійний, і великістю сили своєї він не збереже, —
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
ось око Господнє на тих, хто боїться Його, хто наді́ю на милість Його поклада́є,
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
щоб рятувати життя їхнє від смерти, і щоб за час голоду їх оживляти!
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Душа наша наді́ю склада́є на Господа, — Він наша поміч і щит наш,
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
бо Ним радується наше серце, бо на Ймення святеє Його ми надію кладемо́!
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Нехай Твоя милість, о Господи, буде на нас, коли поклада́ємо наді́ю на Тебе!