< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Ey doğru insanlar, RAB'be sevinçle haykırın! Dürüstlere O'nu övmek yaraşır.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Lir çalarak RAB'be şükredin, On telli çenk eşliğinde O'nu ilahilerle övün.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
O'na yeni bir ezgi söyleyin, Sevinç çığlıklarıyla sazınızı konuşturun.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Çünkü RAB'bin sözü doğrudur, Her işi sadakatle yapar.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Doğruluğu, adaleti sever, RAB'bin sevgisi yeryüzünü doldurur.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Gökler RAB'bin sözüyle, Gök cisimleri ağzından çıkan solukla yaratıldı.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Deniz sularını bir araya toplar, Engin suları ambarlara depolar.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Bütün yeryüzü RAB'den korksun, Dünyada yaşayan herkes O'na saygı duysun.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Çünkü O söyleyince, her şey var oldu; O buyurunca, her şey belirdi.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
RAB ulusların planlarını bozar, Halkların tasarılarını boşa çıkarır.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Ama RAB'bin planları sonsuza dek sürer, Yüreğindeki tasarılar kuşaklar boyunca değişmez.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Ne mutlu Tanrısı RAB olan ulusa, Kendisi için seçtiği halka!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
RAB göklerden bakar, Bütün insanları görür.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Oturduğu yerden, Yeryüzünde yaşayan herkesi gözler.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Herkesin yüreğini yaratan, Yaptıkları her şeyi tartan O'dur.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Ne büyük ordularıyla zafer kazanan kral var, Ne de büyük gücüyle kurtulan yiğit.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Zafer için at boş bir umuttur, Büyük gücüne karşın kimseyi kurtaramaz.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Ama RAB'bin gözü kendisinden korkanların, Sevgisine umut bağlayanların üzerindedir;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Böylece onları ölümden kurtarır, Kıtlıkta yaşamalarını sağlar.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Umudumuz RAB'dedir, Yardımcımız, kalkanımız O'dur.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
O'nda sevinç bulur yüreğimiz, Çünkü O'nun kutsal adına güveniriz.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Madem umudumuz sende, Sevgin üzerimizde olsun, ya RAB!