< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Jublen i HERREN, I rättfärdige; lovsång höves de redliga.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Tacken HERREN på harpa, lovsjungen honom till tiosträngad psaltare.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Sjungen honom en ny sång, spelen skönt med jubelklang.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Ty HERRENS ord är rätt, och allt vad han gör är gjort i trofasthet.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Han älskar rättfärdighet och rätt; jorden är full av HERRENS nåd.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Himmelen är gjord genom HERRENS ord och all dess här genom hans muns anda.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Han samlar havets vatten såsom i en hög; han lägger djupen i deras förvaringsrum.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Hela jorden frukte HERREN; för honom bäve alla som bo på jordens krets.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Ty han sade, och det vart; han bjöd, och det stod där.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
HERREN gjorde hedningarnas råd om intet, han lät folkens tankar komma på skam.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Men HERRENS råd består evinnerligen, hans hjärtas tankar från släkte till släkte.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Saligt är det folk vars Gud HERREN är, det folk som han har utvalt till arvedel åt sig.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Ja, från himmelen skådade HERREN ned, han såg alla människors barn.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Från sin boning blickade han ned till alla dem som bo på jorden,
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
han som har danat allas deras hjärtan, han som aktar på alla deras verk.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
En konung segrar icke genom sin stora styrka, en hjälte räddas icke genom sin stora kraft.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Förgäves väntar man sig seger genom hästar, med all sin styrka rädda de icke.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Se, HERRENS öga är vänt till dem som frukta honom, till dem som hoppas på hans nåd;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
han vill rädda deras själ från döden och behålla dem vid liv i hungerns tid.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Vår själ väntar efter HERREN; han är vår hjälp och sköld.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Ty i honom gläder sig vårt hjärta, vi förtrösta på hans heliga namn.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Din nåd, HERRE, vare över oss, såsom vi hoppas på dig.

< Zabura 33 >